" 'Yan Boko Haram za su dandana kudarsu"

'Yan matan Chibok da aka sace

Asalin hoton, AP

Bayanan hoto, 'Yan matan Chibok da aka sace

Wakiliyar musamman ta majalisar dinkin duniya game da batun yin fyade a lokacin yaki, Zainab Bangura ta ce, masu hannu a satar, mata a yankin arewa maso gabashin Nigeria, za su dandana kudarsu.

Zainab Bangura tana magana ne, bayan da aka sami labarin satar wasu mata akalla ashirin, daga wata rugar Fulani a jahar Borno, kusa da garin Chibok - watau inda 'yan Boko Haram suka sace 'yan matan sakandare fiye da dari biyu da hamsin, kusan watanni biyu kenan.

A cewarta wannan muguwar tabi'a dai ba a Afirka ta tsaya ba.

Alal misali, a lokacin yakin Yugoslavia na farkon shekarun 1990, mata kimanin dubu sittin ne aka yi wa fyade, in ji wani kiyasi na majalisar dinkin duniya.

Haka ma a Syria mutane fiye da dubu talatin da takwas sun nemi taimakon majalisar a bara, bayan an ci zarafinsu.

Zainab Bangura ta ce, duk masu aikata mugayen laifufuka a kan mata, ba za a barsu su tafi salin-alin ba.