Za a kafa kwamitin tattaunawa da Taliban

'Yan Taliban da aka kama
Bayanan hoto, 'Yan Taliban da aka kama

Firaministan Pakistan, Nawaz Sharif ya ce zai kafa kwamiti mai wakilai hudu da zai tattauna da 'yan Taliban na kasar.

A jawabinsa ga majalisar dokoki a karo na uku tun zabensa a bara, Mr Shariff ya ce yanason a samu zaman lafiya a maimakon kaddamar da yaki a kan tsageru.

A bana kungiyar Taliban ta kashe mutane fiye da 100 a hare-haren da ta kai a Pakistan .

Masu sharhi na kallon shugabanni a kasar sun gaza wajen kawo karshen matsalar tsaro.