Boko Haram: An kashe mutane 12 a Borno

Jihar Borno na karkashin dokar ta baci
Bayanan hoto, Jihar Borno na karkashin dokar ta baci

'Yan bindiga da ake zargin 'yan Boko Haram ne sun kashe mutane 12 tare da raunata wasu da dama a wani hari da su ka kaddamar a kauyuka biyu dake jihar Borno dake arewacin Nigeria.

'Yan Boko Haram din a kan babura sun kai hari a kan masu liyafar biki a kauyen Tashan-Alade a daren ranar Asabar sannan kuma a ranar Lahadi su ka kai hari a kauyen Kwajaffa.

Wanda ya shaida lamarin ya bayyanawa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewar 'yan Boko Haram a kan babura sun kaddamar da hare-hare a kan kauyukan kafin su kama gabansu.

A tsakiyar wannan shekarar, Shugaba Goodluck Jonathan ya kaddamar da dokar ta baci a jihohin arewa maso gabas, abinda ya tilastawa 'yan Boko Haram ficewa daga birnin Maiduguri su ka koma kan tsaunukan dake kan iyaka da kasar Kamaru.

A makon da ya gabata ne shugaban kungiyar Boko Haram, Abubakar Shekau a wani bidiyo yace kungiyarsu ce ta kadammar da hari a kan barikin sojoji dake garin Bama a jihar Borno.

Kawo yanzu dai hukumomin tsaro a Najeriyar ba su ce komai ba a kan faruwar al'amarin.