Za a wallafa sunayen masu fyade a India

An dauki matakin ne bayan wani gungun masu aikata laifuka ya yi wa wata yarinya fyade.

Asalin hoton, AP

Bayanan hoto, An dauki matakin ne bayan wani gungun masu aikata laifuka ya yi wa wata yarinya fyade.

Gwamnatin India ta ce tana shirye-shiryen wallafa sunayen duk mutanen da aka samu da laifin yi wa mata fyade.

Gwamnatin ta ce za a wallafa sunayen ne, da suka hada da adireshi da hotunan mutanen.

Ta kara da cewa mutanen da za a wallafa sunayensu za su hada da wadanda shekarunsu ba su kai 18 ba.

Jami'ai a kasar sun ce za a ji ra'ayoyin mutane kan wannan batu.

An dauki matakin ne bayan wani gungun masu aikata laifuka ya yi wa wata yarinya fyade, sanna ya kashe ta a birnin Delhi, fiye da shekara uku da suka wuce.

Lamarin dai ya yi matukar harzuka jama'a.