'Sojojin kasashen duniya za su fice daga Mali'

Dakarun soji a Mali
Bayanan hoto, Dakarun soji a Mali

Ministan harkokin wajen Mali ya ce babu wata hujjar da za ta sa dakarun wanzar da zaman lafiya na kasashen duniya su ci gaba da zama a kasar idan aka ci galaba a yakin da ake yi da 'yan tawayen kasar.

Mista Tiéman Coulibaly ya kara da cewa ba yakin basasa ake yi a Mali ba, illa dai wasu bijirarrun mutane ne suka yi yunkurin tarwatsa kasar.

Tun da farko dai mataimakin shugaban kasar Amurka, Joe Biden, ya shaidawa 'yan jaridu a birnin Paris cewa kasarsa ta amince da bukatar gaggauta kafa dakarun wanzar da zaman lafiya na kasashen duniya karkashin jagorancin kasashen Afrika a Mali.

A ranar Talata wakilan kasashen Turai da Afirka da Majalisar Dinkin Duniya za su yi taro a Brussels don tattaunawa a kan tsaro da kai kayan agaji, da kuma yadda za a kafa sabuwar gwamnatin dimokaradiyya a Mali.