'Mun kama jirgin Burtaniya mai fasakaurin jama'a zuwa Najeriya'

Hadi Sirika

Asalin hoton, Twitter

Bayanan hoto, Ministan sufurin jirage, hadi Sirika ya ce za su hukunta kamfanin jirgin idan sun same shi da laifi
Lokacin karatu: Minti 1

Gwamnatin Najeriya ta ce ta kama wani jirgin sama mallakar wani kamfani da ke Burtaniya bisa zarginsa da yin jigilar Fasinjoji zuwa cikin kasar duk da hanin da aka saka na yin hakan saboda annobar korona.

Ministan sufurin jiragen sama na kasar Hadi Sirika wanda ya sanar da hakan, ya ce an ba jirgin na kamfanin Flair Aviation ne iznin jigila zuwa cikin kasar don taimaka wa wajen ayyukan jinkai, amma kuma ya fake da hakan wajen soma jigila irin ta kasuwanci.

Hadi Sirika ya kara da cewa abin ya ba su mamaki inda suka tsare jirgin sannan ana gudanar da bincike domin gano hakikanin abin da ke faruwa.

Kauce wa X
Ya kamata a bar bayanan X?

Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

Gargadi: Ana iya samun talla wanda ba na BBC ba ne

Karshen labarin da aka sa a X

Ministan dai ya yi zargin abin da ya kira "suna bincike domin gano ko akwai wani abu da ake rufe musu kuma idan muka same kamfanin da laifi za mu hukunta shi daidai gwargwado."

Ya ce gwamnatin Najeriya ta yi shigar burtu inda ta gano yawan kudin da ake biyan jirgin domin kai jama'a Najeriya.

Sai dai kuma ministan bai fadi tsawon lokacin da jirgin ya kwashe yana gudanar da 'haramtattun ayyukan' da gwamantin Najeriyar ke zargin kamfanin.

Har kawo yanzu dai kamfanin Flair Aviation bai ce uffan ba dangane da zargin kuma da zarar ya mayar da martani za mu sanar da jama'a.