KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 30/01/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Juma'a 30 ga watan Janairun 2026.

Rahoto kai-tsaye

Haruna Kakangi, Isiyaku Muhammed da Aisha Babangida

  1. Afrika ta Kudu ta kori jami'in diflomasiyyar Isra'ila

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Gwamnatin Afirka ta Kudu ta kori babban jami’in diflomasiyyar Isra’ila inda ta ba shi sa'o'i 72 ya bar ƙasar.

    Ma’aikatar hulɗa da ƙasashen waje ta ce wannan mataki ya biyo bayan abin da ta bayyana a matsayin “take haƙƙin dokokin diflomasiyya da ba za a yarda da su ba, wanda ke ƙalubalantar ikon mallakar Afirka ta Kudu kai tsaye.”

    A cikin wata sanarwa, hukumomin Afirka ta Kudu sun zargi gwamnatin Isra’ila da amfani da shafukan sada zumunta wajen harin shugaba Cyril Ramaphosa.

    Sannan sun ce ofishin jakadancin Isra’ila bai sanar da su ba lokacin da manyan jami’an Isra’ila suka ziyarci ƙasar.

    Hukumomin sun ƙara da cewa waɗannan ayyuka suna nuna cin zarafin haƙƙin diflomasiyya kuma suna rage amincewar da ake buƙata tsakanin ƙasashen biyu.

    Sakamakon haka, hukumomin suka ayyana cewa ba sa marhaba da jami'in diflomasiyyar na Isra'ila kuma sun ba shi kwanaki uku ya bar ƙasar.

    Dangantaka tsakanin Afirka ta Kudu da Isra’ila ta tsananta tun bayan da ƙasar ta shigar da ƙara a Kotun hukunta manyan laifuka ta duniya ICJ a shekarar 2023, inda take zargin Isra’ila da aikata kisan kiyashi a Zirin Gaza, abin da Isra’ila ta ƙi amincewa da shi.

    BBC ta tuntubi ofishin jakadancin Isra’ila a Pritoria domin jin ta bakinsa.

  2. Sojojin Najeriya sun ceto wani fasto daga hannun ƴanbindiga a Enugu

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Rundunar sojin Najeriya ta ce sojojinta tare da haɗin gwiwar ƴan sa kai ta JTF da sauran hukumomin tsaro sun samu nasarar ceto wani fasto da aka sace, Reverend Johnson Anayo Onugwu, a jihar Enugu.

    An sace faston ne daga gidansa dake al’ummar Ezimo, ƙaramar hukumar Udenu, a daren 29 ga Janairu 2026 da misalin karfe 1:00 na dare, yayin da wasu ‘yan bindiga suka mamaye gidansa.

    Sanarwar da rundunar ta fitar ta ce sojojin da ke garin Udenu sun bi sawun masu garkuwa da fasto ɗin ne bisa bayanan sirri da suka samu inda daga bisani suka yi musayar wuta da ƴanbindigar a al’ummar Okpakeke da ke yankin Itabolo.

    Musayar wutar tsakanin sojojin da ƴanbindigar ya yi sanadin mutuwar ɗaya daga ƴanbindigar lamarin da ya bai wa sojoji damar ceto faston cikin nasara.

    Sanarwa ta kuma ce sojojin sun samu nasarar ƙwato bindiga ƙirar AK-47 da mujallu da harsasa.

    Rundunar ta bayyana cewa, za ta ci gaba da jajircewa wajen kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

  3. Mece ce makomar mataimakin gwamnan Kano?

    ...

    Asalin hoton, Aminu Abdussalam Gwarzo

    A daidai lokacin da aka ci gaba da tattaunawa kan dambarwar siyasar Kano, yanzu haka hankali ya koma kan makomar mataimakin gwamnan jihar, Aminu Abdussalam, wanda har yanzu bai fito ya sanar da komawa jam'iyyar APC ba.

    Tuni dai jam'iyyar NNPP ta yi Allah-wadai da kiran da wasu suke yi ga mataimakin gwamnan ya sauka daga muƙaminsa, inda ta bayyana cewa tikiti ɗaya ne ya kai su kujerar da gwamna.

    Tun farko, an ruwaito kwamishinan yaɗa labarai na jihar Kano, Ibrahim Waiya yana shawartar mataimakin gwamnan jihar, Aminu Abdussalam Gwarzo, da ya yi murabus daga muƙaminsa sakamakon rashin bin gwamna Abba Kabir Yusuf zuwa jam'iyyar APC.

    Ya bayyana haka ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Kano a ranar Alhamis da ta gabata, inda ya ce tafiyar da mulki na buƙatar cikakken aminci da fahimtar juna tsakanin shugabanni.

  4. Amurka ta ayyana Cuba a matsayin barazana ga tsaronta

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban Amurka, Donald Trump ya ayyana Cuba a matsayin barazana ga tsaron ƙasarsa, inda ya sanya hannu kan wata doka ta zartarwa, da ta ba da damar sanya harajin cinikayya ga kowace ƙasa da ke sayarwa ko samar da mai ga ƙasar da ke tsibirin Karebiyan.

    Dokar ta ce cibiyar makamashi mafi girma ta Rasha da ke ƙasashen waje na a kasar ta Cuba, baya ga tallafawa da kuma taimaka wa ƙungiyoyin ta'addanci na ƙasashen waje, kamar Hamas da Hezbollah, da kuma ƙasashen da ke adawa da Amurka, ciki har da Rasha, da China da kuma Iran.

    Gwamnatin Trump na ƙoƙarin toshe duk wasu hanyoyin samar da mai ga Cuba, ciki har da ɗaya daga cikin tsoffin masu samar mata da mai, wato Venezuela

    Wata muhimmiyar ƙasa da itama ke samar da mai ga Cuba ita ce Mexico, wannda ita ma a farkon wannan makon ta ce za ta daina samar da mai ga makwabciyar ta ta.

  5. Chadi da Faransa sun amince da ƙarfafa dangantakar tattalin arziƙisu

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Ƙasashen Chadi da Faransa sun amince da ƙarfafa dangantakar tattalin arzikinsu ta hanyar farfado da haɗin gwiwa bisa ga “girmamawa da muradin juna.” kamar yadda gidan jaridar Alwihda Info mai zaman kansa ya ruwaito.

    Shugaban ƙasar Chadi, Mahamat Idriss Deby Itno, ya gana da takwaransa na Faransa, Emmanuel Macron, a birnin Paris ranar 28 ga Janairu a wata “ziyara ta abota da aiki.” inda ya tafi ƙasar bisa gayyatar Macron.

    “Cikin wannan tsarin, shugabannin ƙasashen biyu sun amince da jerin shawarwari da za su zama taswirar farfado da haɗin gwiwar Faransa da Chadi a fannoni da suke da muradin juna,”.

    Haka kuma, rahoton ya bayyana cewa sun yi alƙawarin ci gaba da tattaunawa don tabbatar da aiwatar da shirin.

    A watan Nuwambar 2024 ne dai dangantaka tsakanin ƙasashen biyu ta yi tsami lokacin da Chadi ta kawo ƙarshen yarjejeniyar soji da Faransa, wanda ya sa Faransa ta janye sojojinta.

  6. Mayaƙan Iswap sun kashe sojojin Najeriya a harin jirage marasa matuƙa

    Army

    Asalin hoton, HQ Nigerian Army

    Rundunar tsaron Najeriya ta tabbatar da cewa mayaƙan Iswap sun kai hari kan sojojinta a garin Sabon Gari da ke jihar Borno a arewa maso gabashin ƙasar.

    Rundunar ta ce an kai harin ne a ranar Alhamis ɗin da ta gabata, kuma ta ƙara da cewa mayaƙan sun yi amfani ne da jirage marasa matuƙa.

    A sanarwar da rundunar tsaron ƙasar ta fitar, ta ce hare-haren sun yi sanadiyar mutuwar wasu sojoji da ba ta bayyana adadinsu ba.

    Mai magana da yawun rundunar, Sani Uba, ya ce an kai harin ne a wani sansanin soji da ke yankin, amma ya ce, "sojojin sun daƙile harin, sannan komai ya lafa."

    A sanarwar da ya fitar a ranar Alhamis, Mr Uba ya ce kafin harin, sojojin na Najeriya sun kai hare-hare a yankin Bulo Dalo, inda a cewarsa suka kashe mayaƙa 12, sannan suka kai wani harin a garin Garno shi ma na jihar ta Borno duka a ranar Laraba, inda a cewarsa a can ma suka kashe mayaƙan guda shida.

    Ya ƙara da cewa sojojin sun ƙwace makamai da alburusai.

  7. Venezuela ta amince da dokar amincewa da masu zuba hannun jari a ɓangaren fetur

    Venezuela

    Asalin hoton, AFP via Getty Images

    Shugabar rikon Ƙwarya ta Venezuela, Delcy Rodriguez, ta sanya hannu kan wata doka da ta ba wa masu sha'awar zuba jari na kasashen waje damar shiga a dama da su, wani abu da canza tsarin gwamnati na shekaru da dama.

    Ana zargin dai Amurka ce ta tilasta yin hakan, bayan ta kama Shugaba Nicolas Maduro a farkon wannan watan, inda yanzu haka yake fuskantar shari'a a ƙasar.

    Shugaba Rodríguez ta bayyana wannan sauyi a matsayin mai cike da tarihi. Yayin da take sanar da matakin ga ƴan ƙasar a wani jawabi da ta gabatar ta talabijin, ta nuna dama can wanda ta gada Nicolas Moduro ya tsara yin hakan kafin a kama shi.

    Tun da farko, Mista Trump ya ba da umarnin bude sararin samaniyar kasar ga jiragen saman yan kasuwa.

  8. Gwamnatin Burkina Faso ta rushe jam'iyyun siyasa a ƙasar

    Traore

    Asalin hoton, Getty Images

    Gwamnatin sojin Burkina Faso ta rushe jam'iyyun siyasa da ƙungiyoyi a ƙasar. Dama can tun a shekarar 2022 ne aka dakatar su, sannan kuma za a miƙa duka ƙadarorinsu zuwa ga gwamnatin ƙasar, kamar yadda kafar gwamnatin ƙasar RTB TV ta ruwaito.

    An amince da dokar rushe jam'iyyun ne a zaman majalisar zartarwar ƙasar, wanda shugaban sojin ƙasar, Ibrahim Traore ya jagoranta.

    Mai magana da yawun gwamnatin ƙasar, Pingdwende Gilbert Ouedraogo ya ce an ɗauki matakin ne bayan nazarin da aka yi kan rahoton binciken da aka gudanar domin inganta harkokin gwamnatin ƙasar, kamar yadda kafar Lefaso.net mai zaman kanta ta ruwaito.

    Kafin juyin mulkin watan Satumban 2022 a ƙasar, akwai jam'iyyun siyasa kusan 100 a ƙasar, inda guda 15 a ciki suke da wakilai a majalisar.

  9. Za mu mayar da martani idan aka kai mana hari - Iran

    Iran da Amurka

    Asalin hoton, EPA

    Shugaba Trump ya ce yana son kauce wa ƙaddamar da harin soja a kan Iran, ko da yake al'amura na iya sauyawa idan har Tehran din ta ci gaba da shirinta na Nukiliya.

    Ya shaida wa 'yan jarida a birnin Washington cewa zai yi magana da Iran din. Tehran dai ta yi barazanar duk wanda ya ce kule, za ta ce masa cas.

    Wani babban jami'in sojan kasar Birgediya Janar Mohammad Akraminia, ya ce karfin sojinsu, ta kai su iya kai hari kan duk wani sansanin sojin Amurkar da ke gabas ta tsakiya.

    Da farko Shugaba Trump ya yi gargaɗin cewa sojojin Amurkar za su kai hari idan Tehran ta kashe fararen hula da ke zanga-zangar adawa da gwamnati ne, kafin daga bisani ya sauya tunani.

  10. Buɗewa

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Juma'a daga wannan shafin namu na BBC Hausa, inda za mu ci gaba da kawo muku labaran kai-tsaye na abubuwan da suke faruwa a Najeriya da sassan duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.