An samu mutum na biyu da ya kamu da coronavirus a Najeriya

Asalin hoton, Getty Images
An samu mutum na biyu da ya kamu da coronavirus a Najeriya.
Hukumar kare yaduwar cututtuka ta Najeriya NCDC ce ta wallafa hakan a shafinta na Twitter a ranar Litinin da misalin karfe 10.30 na safe.
NCDC ta ambato minsitan lafiya na kasar yana mai tabbatar da samun mutum na biyu mai dauke da cutar ta Covid19 a kasar.
An gano mai dauke da cutar ne a jihar Ogun cikin mutanen da aka killace kwanakin baya, "kuma an gano cutar a jikinsa ne a kokarin da muke na gano duk wadanda suka yi alaka da mai dauke da cutar na farko dan kasar italiya."
Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.
Karshen labarin da aka sa a X
NCDC ta ce mutumin na biyu ba shigo da cutar ya yi kasar ba "amma ya yi mu'amala da dan Italiyan da ya shigo da cutar kasar." Hukumar ta ce a yanzu mutumin ya na samun kulawa a asibitin cututtuka masu yaduwa da ke Legas.
A cewar hukumar, sauran mutanen da suka yi mu'amala da mutumin farko a Ogun da Legas za su ci gaba da zama a killace sannan za a yi wa sauran mutanen da ba a yi wa gwaji gwaji ba, har da wadanda suke wasu jihohin.







