Me ya sa kashe-kashen ta'addanci ke ƙaruwa a Najeriya da Nijar?

...

Asalin hoton, Getty Images

Lokacin karatu: Minti 4

Najeriya ce ta shida yayin da Jamhuriyar Nijar ta zo a matsayi na biyar cikin jerin ƙasashen da aka fi kai hare-haren ta'addanaci a duniya, kamar yadda rahoton ayyukan ta'addanci na duniya na shekarar 2025 ya nuna.

Rahoton ya yi nazari ne kan ƙsashe 136, bisa la'akari da abubuwa kamar yawan hare-haren da ka kai, da waɗanda hare-haren suka rutsa da su da kuma mutanen da aka yi garkuwa da su.

Rahoton, wanda cibiyar zaman lafiya da tattalin arziƙi ta duniya ta fitar a ranar 5 ga watan Mayu ya nuna cewa Najeriya ta samu ci baya daga matsayi na takwas da take a rahoton da aka fitar cikin shekarun 2024 da 2023.

Najeriya ta zo ta shida ne bayan Jamhuriyar Nijar da ake a matsayi na biyar, Mali a matsayi na huɗu, Syria a matsayi na uku, Pakistan a matsayi na biyu, sai Burkina Faso a matsayi na ɗaya.

Rahoton na wannan karo ya nuna cewa a Najeriya an samu kashe-kashe masu alaƙa da ta'addanci guda 565 a shekarar 2024, wanda hakan ya zarce na shekaru biyu da suka gabata.

Wannan na zuwa ne duk kuwa da cewa rahoton ya nuna cewa an samu raguwar kashe-kashen ta'addanci a duniya cikin shekarar ta 2024.

Najeriya ta daɗe tana fama da hare-hare na ta'addanci, musamman daga mayaƙan ƙungiyar Boko Haram, wadda ta shafe sama da shekara 10 tana gudanar da ayyukanta a yankin arewa maso gabashin ƙasar.

Duk da cewa an raunana ƙungiyar sosai, amma a shekarar da ta gabata an ga farfaɗowar hare-harenta a yankunan jihar Borno, inda ta kai harin ƙunar baƙin wake a garin Gwoza, wanda ya yi ɓarnar da aka daɗe ba a gani ba.

Haka nan mayaƙan ƙungiyar sun kai farmaki da dama a kan sojoji da kuma kashe manoma da masunta a ƙauyuka, lamarin da ya haifar da tsoro a zukatan al'umma.

Abin da rahoton ya ce kan yankin Sahel

...

Asalin hoton, Boko Haram

Tsallake Whatsapp
Tasharmu ta WhatsApp

Yanzu za ku iya samun labaran BBC Hausa kai-tsaye a wayoyinku.

Latsa nan domin shiga

Karshen Whatsapp

Rahoton ya nuna cewa a karo na biyu, Sahel ne yankin da ya fi kowane a duniya fama da hare-haren ta'addanci.

Yankin ne ya samu fiye da rabi na adadin mutanen da aka kashe ta hanyar hare-haren ta'addanci a faɗin duniya, kamar yadda rahoton ta bayyana.

Rahoton ya nuna cewa biyar da cikin ƙasashe 10 da ta'addanci ya fi yi wa katutu a duniya suna a Sahel ne - makekekn yanki mai rairaiyi wanda ya tashi daga tekun Atlantika a yammacin Afirka zuwa Tekun Maliya da ke gabashin nahiyar.

Ƙasashen Burkin Faso, wadda ta zo ta ɗaya a jerin, da Mali da kuma Jamhuriyar Nijar su ne waɗanda suka fi shan wahala.

Rikicin masu tayar da ƙayar baya da ya ɓarke a Mali, shekaru 10 da suka gabata ya yadu zuwa Burkin Faso da Jamhuriyar Nijar masu maƙwaftaka.

Manyan ƙungiyo biyu da ake ɗora wa laifin kai hare-haren su ne IS da kuma wata ƙungiya mai alaƙa da Alqaeda a ƙasar Mali.

Rahoton ya nuna cewa cibiyar hare-haren ta'addanci ta tashi daga Gabas ta tsakiya zuwa yankin Sahel na nahiyar Afirka.

Duk da cewa yawan mutanen da aka kashe sanadiyyar hare-haren ta'addanci ya ƙaru a Najeriya a 2024, amma ƙasar na daga cikin waɗanda aka fi samun raguwar irin waɗannan kashe-kashe a tsawon shekaru.

A 2014 ne aka samu irin waɗannan kashe-kashe mafi yawa a ƙasar, inda aka kashe mutum 2,101 sanadiyyar hare-haren ta'addanci, inda kuma yawan ya yi ƙasa sosai zuwa kashe-kashe 392 a 2022, wanda shi ne mafi ƙaranci tun daga 2011.

Sai dai irin waɗannan kashe-kashe sun ƙaru da kashi 34 cikin ɗari a 2023, inda aka kashe mutum 533, sai kuma ya ƙaru zuwa 565 a 2024.

Ƙasashe 10 da ta'addanci ya fi yi wa illa

Burkina Faso ce ta zamo ta farko a jerin cikin shekara biyu a jere:

1 - Burkina Faso

2 - Pakistan

3 - Syria

4 - Mali

5 - Jamhuriyar Nijar

6 - Najeriya

7 - Somaliya

8 - Isra'ila

9 - Afghanistan

10 - Kamaru

Rahoton na ƙasashen da ta'addanci ya fi shafa ya ce ƙasashen da aka fi samun ƙaruwar kashe-kashe masu alaƙa da ta'addanci tun daga 2007 su ne Pakistan da Syria da kuma Mali.

Iraqi kuma ita ce ƙasar da aka fi samun raguwar irin waɗannan kashe-kashe, inda ya ragu da kashi 99 cikin ɗari daga shekarar 2007, inda aka samu kisan mutane 6,249 zuwa 59 a 2024.

Ƙasashen Afghanistan da kuma Thailand na cikin jerin ƙasashen waɗanda suka samu raguwar kashe-kashe sanadiyyar ta'addanci.