KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 15/01/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Alhamis, 15 ga watan Janairun 2026.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida da Haruna Kakangi

  1. Gwamnatin Sokoto ta amince da kafa cibiyar jami’an tsaro a yankin Tidibale

    Gwamnan jihar Sokoto, Ahmad Adamu

    Asalin hoton, Sokoto State Government

    Gwamnatin jihar Sokoto ta sanar da amincewa da kafa cibiyar tabbatar da tsaro a yankin Tidibale da ke jihar, inda ake zargin ‘yan bindiga da yi wa al’umma barazana tare da tursasa ma wasu barin muhallansu.

    Gwamnatin ta bayyana haka ne a cikin wata sanarwa da ta fitar, wadda ta samu sa hannun Abubakar Bawa, shugaban sashen yada labaru na ofishin gwamnan jihar.

    Sanarwar ta ce samar da cibiyar tabbatar da tsaron za ta taimaka wa ayyukan wata irin ta a karamar hukumar ta Isa.

    Haka nan sanarwar ta karyata wani bidiyo da ake yadawa a shafukan sada zumunta da ke cewa mutanen yankin Tidibale ne da ‘yan bindiga suka kora daga kauyukansu.

    A cewar sanarwar mutanen da aka gani a bidiyon, su ne wadanda gwamnati ta kwashe daga kauyukan yankin na Tidibale zuwa cibiyar karamar hukumar bayan samun bayanai na tsaro.

    “Tabbas mutanen Tidibale ne, amma ba yan bindiga me suka koro su ba,” a cewar sanarwar.

    “Mutane ne da aka kwashe su na wucin-gadi zuwa cibiyar karamar hukuma bayan rade-radi game da yiwuwar fuskantar hare-hare daga ‘yan bindiga.

    “Haka nan kuma an riga an mayar da mutanen zuwa kauyensu na Tidibale, inda kuma jami’an tsaro ke aikin tabbatar da doka da hana ayyukan ‘yan bindiga,” a cewar sanarwar.

    A baya-bayan nan ne rahotanni daga jihar ta Sokoto suka bayyana yadda mutane ke guje wa kauyukansu sanadiyyar barazanar ayyukan ‘yan bindiga.

    Sokoto na cikin jihohin arewa maso yammacin Najeriya da suka daɗe suna fama da matsalar tsaro ta kungiyoyin ‘yan bindiga masu kisa da kuma garkuwa da mutane domin neman kuɗin fansa.

  2. Abubuwa huɗu da suka hana magance matsalar tsaro a Najeriya - C.G. Musa

    ...

    Yayin da matsalar tsaro ta ƙi ci ta ƙi cinyewa a sassan Najeriya, ministan tsaron ƙasar, Janar Christopher Musa, ya ce gwamnati na bin tsarin da ya dace wajen magance matsalar, inda ta ke haɗa ayyukan soji da kuma sauran dabaru.

    A wata hira da ya yi da BBC, Janar Musa mai ritaya ya amince cewa har yanzu akwai rina a kaba a yaƙin da gwamnatin ke yi da matsalar inda ya jaddada buƙatar tabbatar da tsaron kan iyakokin Najeriya don hana zirga-zirgar masu aikata laifuka.

    Najeriya na fuskantar matsalar tsaro ta Boko Haram wadda ta shafe sama da shekara 15 tana fama da ita. Har yanzu ƙungiyar na da ƙarfin kai hare-hare nan da can, tare da hana manoma da masunta gudanar da ayyukansu.

    Matsalar ƴan awaren Ipob, ita ma ta ƙi ci ta ƙi cinyewa, inda ƴan bindigan ke ƙaƙaba wa fararen hula dokoki da kuma ya wa mutane kisan ɗauki ɗaiɗai a kudu maso gabashin ƙasar.

    A arewa ta tsakiyar ƙasar ana ci gaba da fuskantar daɗaɗɗiyar matsalar rikici tsakanin manoma da makiyaya waɗanda ke hanƙoron samun filayen gudanar da sana'o'insu.

  3. 'Tsaikon wajen isar da kayan aiki ya janyo jinkiri a zaɓen Uganda'

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Hukumar zaɓe ta Uganda ta ce matsalar tsaiko wajen isar da kayan aiki ya janyo jinkiri a zaɓen shugaban ƙasa da na ƴan majalisu da ake yi.

    Sun ɗaura alhakin jinkirin sa'oi huɗu da aka samu kan na'urorin kaɗa ƙuri'a da suka ƙi yin aiki da kuma rashin samar da wasu kayyayakin aikin.

    Rahotanni sun bayyana cewa wasu masu zaɓen sun bar rumfunan zaɓe ba tare da jefa ƙuriar su ba.

    Shugaba Yoweri Museveni, wanda ke takara domin zama shugaba a karo na bakwai, ya ce shi ma ya samu matsala wajen kaɗa ƙuri'arsa.

    Ya na takara ne da mawaƙi Bobi Wine, wanda ke da tarin magiya baya a sassa da dama na babban birnin ƙasar Kampala.

  4. 'Matashin da aka kama lokacin zanga-zanga a Iran ba zai fuskanci hukunci ba'

    Shugaba Trump ya yi maraba da rahotannin da ke cewa matashin nan da aka kama lokacin zanga zanga a Iran ba zai fuskanci hukuncin kisa ba kamar yadda aka yi ta fargaba.

    Sashen shari'a na Iran ya ce ba a yanke wa Erfan Soltani hukuncin kisa ba, kuma laifukan da ake tuhumarsa da su ba su da hukuncin kisa.

    Mista Trump ya wallafa a shafinsa na sada zumunta cewa wannan labari ne mai kyau, kuma yana fatan za a ci gaba a haka.

    Ya ce mun samu labarin cewa an daina kashe mutane a Iran, kuma an janye maganar hukuncin kisa, amma idan aka yi hakan za mu fusata sosai.

    Tun da farko ya yi barazanar ɗaukar mummunar mataki kan Iran idan ta fara zartar da hukuncin kisa kan masu zanga-zanga.

  5. Za mu gina katanga a iyakokin Najeriya- Ministan tsaro

    ...

    Ministan tsaron Najeriya, Christopher Musa, ya bayyana cewa yana da niyyar gina katanga a iyakokin Najeriya inda ya ce hakan zai taimaka wajen hana miyagun mutane shiga ƙasar.

    A hirarsa da BBC, Ministan tsaron ya bayyana cewa rashin tsaro a iyakoki na bai wa 'yan bindiga damar tsallakawa cikin ƙasar daga ƙasashen da ke maƙwaftaka.

    Ya ce katangar za ta taimaka wajen hana "miyagu" shiga sannan za su yi amfani da na'urori domin tsare wuraren da ba za a iya yin katanga ba.

    “Watakila ba za mu iya samun katanga a ko’ina ba, saboda wasu wurare akwai ruwa inda ba za a iya gina katanga ba. Amma akwai fasaha da dama da za mu iya amfani da su cikin tsari. Wasu daga cikin waɗannan fasahar na iya kunna ƙararrawa da zarar an ƙetare iyaka, wanda zai ba mu damar daukar mataki nan da nan,” in ji Musa.

    “Muna duba wannan al’amari daga kowane ɓangare." in ji shi. Najeriya na da fiye da kilomita 4,000 na kan iyaka, amma ministan wanda ya taɓa zama shugaban Hafsan Sojojin Najeriya, ya ce gina katanga a dukkan iyakokin abu ne mai yiwuwa.

    Gwamnatin Najeriya ta bayyana sau da yawa cewa iyakokin ƙasar na daga cikin manyan dalilan ƙaruwar rashin tsaro.

  6. Cuba za ta karɓi gawarwarkin sojojinta da aka kashe a Venezuela

    Gawarwakin sojojin Cuba guda talatin da biyu da jami'an tsaro suka kashe a Venezuela a lokacin da Amurka ta kama tsohon shugaban Venezuela Nicolas Maduro za su isa Havana nan ba da jimawa ba.

    Ƴan Cuban na aiki ne a matsayin masu kare Maduro wanda sojojin Amurka suka ɗauke da ƙarfin tsiya zuwa New York domin ya fuskanci shari'ar kan tuhumarsa da laifin safarar ƙwayoyi.

    Za a tarbi gawarwakin da tarba ta gimamawar soji.

    Ana ganin wannan ne adadi mafi yawa na ƴan Cuba da sojojin Amurka suka kashe tun bayan mamayar alif dari tara da sittin da ɗaya.

    Venezuela ta ce mutane fiye da ɗari aka kashe a ƙasar a lokacin da Amurka ta kai harin.

    Cuba da Venezuela sun kasance ƙawaye na tsawon lokaci, inda Cuba ke matuƙar dogaro da man Venezuela, yayin da ita kuma ke taimaka ma Venezuela a fannin tsaro.

  7. Harin ƴan aware a yankin Anglophone na Kamaru ya kashe mutane 14

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Ƙungiyoyin kare haƙƙin bil'adama da masu fafutukar kare al’umma sun yi allawadai da harin da ake zargin ƴan awaren Anglophone ne suka kai a ƙauyen Fulani a arewa maso yammacin Kamaru, wanda ya kashe mutane 14 a ranar Laraba.

    Gwamnan yankin, Adolphe Lele Lafrique ya ce maharan sun buɗe wuta yayin da yawancin mazauna yankin ke barci tare da ƙona gidaje da kashe dabbobi sannan sun kuma sace babura.

    Mutum 10 kuma sun jikkata a harin ciki har da yara biyu, waɗanda ake kula da su a asibiti.

    Lauyan kare hakkin ɗanadam, Felix Agbor Balla ya ce kai wa fararen hula hari laifi ne mai tsanani a ƙarƙashin dokar ƙasashen duniya, yana mai kira a gudanar da bincike mai gaskiya da adalci don gano masu laifin.

    Tun daga shekarar 2017 ne rikici tsakanin ƴan aware da gwamnati a yankunan Anglophone biyu na Kamaru ya kashe kimanin mutum 6,000 tare da tilastawa sama da rabin miliyan barin gidajensu.

  8. X zai dakatar da Grok AI daga ƙirƙirar hotunan batsar mutane

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Shafin sada zumunta na Elon Musk, X, ya sanar da sabbin matakai da zai ɗauka don dakatar da manhajarsa ta fasahar gagarabadau wata Grok AI daga ƙirƙirar hotunan batsar mutane ba tare da neman yardarsu ba, musamman hotunan da ke bayyana surar mutane cikin kaya ko yanayi na sirri.

    Ana ci gaba da samun suka daga sassan duniya kan yadda ake amfani da manhajar wajen ƙirƙirar hotunan batsa na mata da yara.

    Sababbin matakan za su shafi duk masu amfani da shafin X, ciki har da waɗanda ke biyan kuɗin amfani da shi.

    Matakin na zuwa ne bayan babban mai gabatar da ƙara a California ya bayyana cewa jihar za ta yi bincike kan yadda ake amfani da manhajar Grok wajen ƙirƙirar hotunan karya da kuma abubuwan da suka saɓa doka.

    Haka kuma, Malaysia da Indonesia sun toshe hanyoyin samun manhajar, yayin da Firaministan Birtaniya ya yi barazanar hana shafin ko kuma yin masa tarar kuɗi saboda irin abubuwan da ake amfani da manhajar wajen ƙirƙira.

    Wannan matakin na X na nuni da kokarin dakile amfani da AI wajen karya haƙƙokin mutane da kuma kare martabar masu amfani da shafin.

  9. Masu zaɓe sun fara kaɗa ƙuri’a a zaɓen shugaban ƙasar Uganda

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Masu zaɓe a Uganda sun fara kaɗa ƙuri'a a a zaɓen shugabancin ƙasar da shugaba Yoweri Museveni, ke neman ta-zarce a wa'adi na bakwai, bayan kusan shekara 40 a kan mulki.

    Sama da 'yan Uganda miliyan 20 ne ke kada kuri'aru a ɗaya daga cikin zabukan da aka fi sanya wa ido.

    Babban mai ƙalubalantarsa, shi ne mawaƙin da ya juye ya zama ɗan siyasa - Robert Chagulanyi wanda aka fi sani da Bobi Wine, da ke takara a karo na biyu.

    Zuwa jibi Asabar da rana ake sa ran bayyana wanda ya yi nasara a zaɓen.

    Ofishin kare hakkin dan'Adam na mjalaisar Dinkin Duniya, ya ce ana zaɓen ne cikin yanayi na tsoro da fargaba, kasancewar an tsare ɗaruruwa magoya bayan ɗan hamayyar, kafin zaɓen.

    Hukumomin ƙasar sun katse hanyoyin intanet a faɗin kasar saboda abin da suka kira damuwa kan yaɗa bayanai na karya da kuma tashin hankali.

  10. Ba zan koma APC ba sai an faɗa min matsayina a jam'iyya - Kwankwaso

    ...

    Asalin hoton, Kwankwaso/Facebook

    Jagoran jam’iyyar NNPP kuma tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya ce ba zai koma jam’iyyar APC ba sai an fayyace masa matsayinsa a jam'iyyar kuma sai an dawo da takardun manufofin da suka rubuta kan yadda za a tafiyar da rayuwar talakawan Najeriya.

    Kwankwaso ya jaddada cewa dole ne sai an fayyace masa matsayin magoya bayansa da kuma gwamnatin jihar Kano kafin ya yanke duk wata shawara.

    Kwankwaso ya bayyana hakan ne a ranar Laraba a gidansa da ke Miller Road a Kano, yayin da yake karɓar shugabanni da magoya baya daga ƙananan hukumomin Rano da Dawakin Tofa, tare da wasu mambobin tafiyar Kwankwasiyya da suka sake jaddada biyayyarsu ga jam’iyyar NNPP.

    Jagoran ya bayyana cewa "Idan har zan koma jam'iyyar APC dole ne a sanar da ni matsayi na a cikin jam’iyyar, sai an faɗa mana abubuwan da za a yi mana sannan kuma sai mun san matsayin jihar Kano da magoya bayanmu."

    Kwankwaso ya bayyana cewa burinsa shi ne kare muradun al’umma, musamman talakawa, tare da tabbatar da cewa duk wata tafiya ta siyasa za ta amfanar da magoya baya da kuma jama’ar jihar Kano gaba ɗaya.

    Wannan furuci na Kwankwaso na zuwa ne a daidai lokacin da ake ta raɗe-raɗin yiwuwar sauya sheƙar gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, zuwa jam’iyyar APC.

  11. Shugabar riƙon-ƙwaryar Venezuela ta tattauna da Trump kan alaƙar ƙasashen biyu

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugabar rikon-kwarya ta Venezuela Delcy Rodriguez, ta yi wata tattaunawa mai tsawo da armashi, ta waya da Shugaban Amurka, Donald Trump, inda suka tattauna kan alakar kasashensu biyu.

    Bayan tattaunawar ta waya, Trump, ya ce a yanzu an samu fahimtar juna sosai tsakanin Amurka da Venezuela - suna ɗasawa, har ma ya bayyana shugabar a matsayin mai ban mamaki.

    Wannan tattaunawar ita ce ganawa ta farko da aka sani tsakanin su tun bayan hamɓarar da tsohon shugaban ƙasar, Nicolás Maduro.

    Rodríguez ta karɓi ragamar mulkin Venezuela a matsayin shugabar rikon-kwarya ne bayan da Amurka ta kame tsohon shugaban ƙasar Maduro a farkon watan Janairu ta kai shi kasarta, ta gurfanar da shi gaban sharia kan zargin safarar miyagun kwayoyi lamarin da ya janyo sabon yanayin siyasa a Caracas.

  12. Iran ta ce ba ta da shirin kashe masu zanga-zanga

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi, ya ce gwamnatin ƙasarsa ba ta da wani shiri na aiwatar da hukuncin kisa kan mutanen da aka kama bisa zargin shiga zanga-zanga.

    Araghchi ya bayyana hakan ne yayin wata hira da ya yi da kafar yaɗa labarai ta Fox News, inda ya kuma yi gargaɗi ga Shugaban Amurka, Donald Trump, da kada ya sake aikata abin da ya kira kuskuren da aka yi a bara, lokacin da Amurka ta kai hare-haren sama kan wasu muhimman tashoshin nukiliyar Iran a watan Yuni.

    Trump dai ya yi barazanar ɗaukar tsauraran matakai idan har Iran ta aiwatar da hukuncin kisa kan masu zanga-zanga. Sai dai daga baya ya ce an tabbatar masa cewa Iran ta dakatar da kisan masu zanga-zangar.

    Sai dai har yanzu tambayar har yanzu ita ce: ko Trump yana jan lokaci ne, ko kuwa yana ƙoƙarin shammatar Iran—kuma mene ne ainihin lissafinsa a wannan lokaci?

    A halin da ake ciki, a ranar Laraba, Amurka da Birtaniya sun janye wasu daga cikin sojojinsu daga wani muhimmin sansani a ƙasar Qatar, lamarin da ke ƙara tayar da hankalin jama’a kan yiyuwar Amurka ta sake kai hari a yankin.

  13. 'Babu sauran kulawa da gwamnati ke bai wa iyalin Tafawa Balewa'

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Yayin da ake cika shekara 60 da juyin mulkin soji na farko a Najeriya, BBC ta kai ziyara inda aka binne gawar mutum mafi girman muƙami da aka kashe a lokacin juyin mulkin.

    Abubakar Tafawa Ɓalewa shi ne Firaiministan Najeriya na wancan lokaci, kuma yana cikin waɗanda sojojin suka hallaka a shekarar 1966, baya ga Firimiyan jihar Arewa da na Yamma da kuma manyan sojoji da masu riƙe da muƙaman gwamnati.

    Shi ne juyin mulkin da ya kawo ƙarshen jamhuriya ta farko a Najeriya, wadda ta ƙunshi fitattun mutane da suka yi fafutikar samun ƴancin kan ƙasar.

    An binne marigayin ne a garin Bauchi da ke jiharsa ta asali a arewa maso gabashin Najeriya.

    Cikin iyalan Tafawa Ɓalewa da BBC ta zanta da su, akwa jikan marigayin, Abubakar (Billy) Tafawa Ɓalewa wanda ya nuna takaici kan halin da kabarin kakan nasa ke ciki da kuma kuma iyalansa.

  14. Assalamu alaikum

    Masu bin shafin BBC Hausa kai-tsaye barkanmu da safiyar wannan rana ta Alhamis.

    Kamar kullum, yau ma za mu kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Aisha Babangida da Abdullahi Bello Diginza ke fatan sake kasancewa da ku a daidai wannan lokaci.

    Za ku iya leƙawa shafukan sada zumuntanmu na intanet, da facebook da X da kuma whatsapp domin karanta sauran labarai da kallon bidiyo da tafka muhawara.