Wolves tasha kashi a gida a hannun Manchester City

Manchester City players celebrate

Asalin hoton, Getty Images

An wallafa

Manchester City ta fara kakar bana ta Premier League da kafar dama, bayan da ta doke Wolves da ci 3-1 a karawar da suka yi a Molineux.

City ta fara cin kwallo ta hannun Kevin de Bruyne, sannan dan kwallon tawagar Ingila Phil Foden ya kara na biyu.

City ta yi ta kai hare-hare, amma haka suka je hutu babu wacce ta zura kwallo a raga.

Daga baya ne Raul Jimenez ya zare kwallo daya daga biyun da aka zura musu, sai dai daf da za a tashi daga wasan Gabriel Jesus ya ci wa City na uku.

Da wannan sakamakon Wolves za ta ziyarci West Ham United a karawar gaba ranar Lahadi 27 ga watan Satumba.

Ita kuwa Manchester City za ta karbi bakuncin Bournemouth a wasan zagaye na uku a Caraboa Cup ranar Alhamis 24 ga wata.

Daga nan ne ta karbi bakuncin Leicester City a wasanta na mako na biyu a gasar Premier League ranar Lahadi 27 ga watan Satumba.