KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 03/03/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Talata 3 ga watan Maris 2026.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida, Haruna Kakangi da Abdullahi Bello Diginza

  1. Trump ya soki firaiministan Birtaniya kan 'rashin taimaka' wa Amurka

    Donald Trump da Keir Starmer

    Asalin hoton, Reuters

    Bayanan hoto, Shugaban Amurka Donald Trump da Firaiministan Birtaniya Keir Starmer

    Shugaban Amurka, Donald Trump, ya soki firaiministan Birtaniya, Keir Starmer, kan abin da ya kira rashin taimaka wa Amurka a hare-haren da ta kai kan Iran.

    A wata hira ta wayar tarho da jaridar The Sun, Trump ya ce Starmer “bai taimaka ba. Ban taɓa tunanin zan ga hakan ba. Ban taba tunanin zan ga hakan daga Birtaniya ba.”

    Ya kara da cewa wannan abin takaici ne ganin dangantakar ƙasashen biyu.

    A ranar Litinin, Starmer ya shaida wa majalisar dokokin Birtaniya cewa gwamnatinsa “ba ta goyon bayan sauya mulki ta hanyar hare-hare ba."

    Da farko dai Birtaniya ba ta amince Amurka ta yi amfani da sansanoninta wajen kai hari kan Iran ba, amma daga baya ta buɗe sansanonin nata domin abin da ta kira hare-haren kariya kan wasu wurare a Iran.

    Trump ya kuma ce Faransa ta nuna goyon baya sosai, yana mai cewa, “Faransa ta yi abin kirki.

    Sauran ma sun yi abin kirki. Amma Birtaniya ta bambanta da sauran.”

  2. Muna da isassun makaman yaƙi 'har abada' - Trump

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban Amurka, Donald Trump, ya ce ƙasarsa na da isassun makaman yaƙi da za a iya amfani da su “har abada”, yana mai jaddada cewa Amurka a shirye take ta yi nasara a duk wani rikici.

    Trump ya bayyana hakan ne a wani saƙo da ya wallafa a dandalin sada zumunta na Truth Social, inda ya yi magana kan abin da ya kira tarin makaman da Amurka ke da su.

    Ya rubuta cewa, ana iya gudanar da yaƙe-yaƙe na dogon lokaci ta amfani da irin waɗannan makamai kaɗai.

    Ya kuma ƙara da cewa, “Amurka na da tarin makamai marasa iyaka, kuma a shirye take ta yi nasara babba,”.

    Trump ya kuma zargi tsohon shugaban ƙasar, Joe Biden, da bai wa Ukraine makaman Amurka masu matuƙar ƙarfi da yawa.

    A ƙarshen wa’adin mulkinsa na shekara huɗu, Biden ya amince Ukraine ta yi amfani da makamai masu linzami na dogon zango irin su ATACMS, waɗanda ke iya kai hari har nisan mil 190, kimanin kilomita 300.

  3. Harin Iran ya lalata sansanin sojin saman Amurka a Bahrain

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Rahotanni na cewa wani hari da Iran ta kai ya lalata babban sansanin sojin saman Amurka da ke ƙasar Bahrain.

    Hotuna da bidiyo da kamfanin dillancin labarai na Fars News Agency, wanda ke da alaƙa da dakarun juin juya halin Iran IRGC ya wallafa, sun nuna abin da ya yi kama da jerin makamai masu linzami na faɗowa kan wasu wurare daga nesa tare da fashewa.

    Rahoton ya yi iƙirarin cewa harin jiragen sama marasa matuƙa da makamai masu linzami na IRGC ya lalata wani ginin da ma’aikatar Amurka a yankin Sheikh Isa na Bahrain, tare da haddasa fashewar tankunan mai.

    Har zuwa yanzu, Amurka ba ta fitar da wata sanarwa kan waɗannan rahotanni ba.

    A baya dai an ga hayaƙi na tashi daga wani sansanin sojan ruwa da Amurka ke gudanarwa a Bahrain.

    Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka ta ba ‘yan ƙasarta umarnin su fice daga Bahrain nan take, tare da wasu ƙasashe kusan goma sha biyu a yankin Gabas ta Tsakiya, saboda matsalar tsaro da ke ƙara kamari.

  4. An kai hari kan ofishin jakadancin Amurka a Saudiyya

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Ma’aikatar Tsaron Saudiyya ta tabbatar da cewa an kai hari kan ofishin jakadancin Amurka da ke birnin Riyadh da jiragen sama marasa matuƙa guda biyu, lamarin da ya haddasa wata ƙaramar gobara da kuma lalacewar kayayyaki kaɗan a ginin.

    A cikin sanarwar da ma’aikatar ta wallafa a shafinta na X, ta ce bisa ƙiyasin farko, harin bai yi sanadiyyar asarar rai ba, amma ya janyo ɓarnar da ba ta wuce iyaka ba a cikin ginin.

    A nasa bangaren, ofishin jakadancin Amurka a Saudiyya ya fitar da umarnin kowa ya zauna a inda yake ga ma’aikatansa da ke biranen Jeddah da Dhahran tare da Riyadh.

    Haka kuma ya bayyana cewa zai takaita duk wata tafiya da ba ta zama dole ba zuwa sansanonin soji a yankin.

  5. Iran na ci gaba da luguden wuta kan Isra'ila da sansanonin sojin Amurka

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Iran na ci gaba da yin luguden wuta kan Israila da sansanonin sojin Amurka a ƙasashen gabas ta tsakiya.

    Saudiyya ta ce wasu jirage marasa matuƙa biyu na Iran din sun kai hari kan Ofishin Jakadancin Amurka da ke babban birnin ƙasar, Riyadh.

    Ma’aikatar tsaron ƙasar ta ce ta samu nasarar kakkaɓo wasu jirage marasa matuƙa guda takwas da ke kan hanyarsu ta zuwa babban birnin, da kuma birnin Al-Kharj da ke kusa.

    Ofishin Jakadancin Amurka ya bai wa ‘yan ƙasarsa da ke zaune a masarautar shawarar su nemi mafaka a inda suke.

    Ƙasashen Qatar da Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa da kuma Isra’ila su ma sun bayar da rahoton cewa makamai masu linzami na ta yawo a sararin samaniyarsu.

    Yanzu haka Amurka ta bukaci yan kasarta da ke zaune a kasashe goma sha biyu na yankin su fice cikin gaggawa.

  6. Yawan sojojin Amurka da aka kashe a yaƙin Iran ya kai 6

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Rundunar sojin Amurka ta tsakiya, wato Centcom ta ce adadin sojojin Amurka da suka mutu a yaƙin Iran ya kai shida.

    A cikin sanarwar da rundunar ta fitar, ta bayyana cewa sojojinta sun gano gawarwakin wasu sojoji biyu da a baya ba a san inda suke ba, daga wani gini da aka kai wa hari a farkon luguden wutar da Iran ta soma kai wa a yankin.

    Sanarwar ta kara da cewa yaƙi na ci gaba da gudana, duk da asarar da aka samu.

    Rundunar ba ta yi ƙarin bayani kan inda harin ya fi ƙamari ba ko kuma ko akwai ƙarin sojojin da suka jikkata.

    Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da rikici ke kara tsananta a yankin ƙasashen gabas ta tsakiya inda ake ci gaba da musayar wuta tsakanin Amurka da Isra'ila da Iran

  7. Mutum shida da za su iya maye gurbin Ayatollah Ali Khamenei

    ....

    Asalin hoton, BBC Monitoring

    Kamar yadda kundin tsarin mulkin Iran ya tanada, Majalisar Masana ta ƙasar – wadda ta ƙunshi manyan malaman addini 88 – ce za ta zaɓi mutumin da zai zamo sabon jagoran addinin ƙasar.

    Ana zaɓen wakilan majalisar malaman Iran ne a duk shekara takwas, kuma dole ne sai Majalisar Magabata ta ƙasar ta tantance su.

    Masu goyon bayan Ali Khamenei ne suka lashe dukkanin kujerun majalisar a zaben shekara ta 2024, inda daga baya aka samu giɓi a kujeru huɗu bayan mutuwar wakilansu – cikin har da Ebrahim Raisi, waɗanda za a cike gurbinsu a zaɓen cike gurbi da za a yi a watan Mayun 2026.

    Sashe na 111 na kundin tsarin mulkin ƙasar ya tanadi cewa a samar da wata majalisa ta mutum uku ta wucin-gadi, wadda za ta gudanar da al'amuran ƙasar kafin zaɓen sabon jagoran addini.

    Kwamitin riƙon-ƙarywar zai ƙunshi shugaban ƙasa Massoud Pezeshkian, da babban alƙalin alƙalan ƙasar Gholamhossein Mohseni Ejei da kuma malami masanin shari'a guda ɗaya daga Majalisar Magabata ta ƙasar.

  8. Assalamu alaikum

    Masu bin shafin BBC Hausa kai-tsaye barkanmu da safiyar wannan rana ta Talata.

    Kamar kullum, yau ma za mu kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Aisha Babangida da Abdullahi Bello Diginza ke fatan sake kasancewa da ku a daidai wannan lokaci.

    Za ku iya leƙawa shafukan sada zumuntanmu na intanet, da facebook da X da kuma whatsapp domin karanta sauran labarai da kallon bidiyo da tafka muhawara.