Kungiyar IS ta fille kawunan 'yan Taliban

Asalin hoton, AP
Dakarun Afghanistan sun ce mayakan kungiyar IS sun fille kawunan wasu 'yan Taliban su 10 a yankin gabashin kasar.
Ana hasashen cewa wannan ne karon farko da aka hallaka mayakan Taliban ta wannan hanyar.
An samu bayanan kisan ke a wata wasika ta sirri da aka aika wa manema labarai bisa kuskure.
Fille kawunan 'yan Taliban din na zuwa ne bayan makonni da aka shafe ana fafatawa tsakanin kungiyoyin biyu a lardin Achin da ke kusa da kan iyaka da kasar Pakistan.
A waje daya kuma Amurka ta ce an hallaka mayakan IS 10,000 tun lokacin da sojojin kawancen kasashe suka soma fafatawa da 'yan IS a kasashen Iraki da Syria.







