INEC za ta fara raba katin zabe

Asalin hoton, b
A gobe Juma'a ake sa ran hukumar zaben Najeria mai zaman kanta INEC za ta fara raba katin zabe na dun-dundun a wasu jihohin kasar.
A baya dai hukumar ta shirya raba katunan ne a jihohi 13, amma a yanzu hukumar ta ce za a bayar da su ne a karshen makon nan a wasu jihohi biyar.
Sannan za kuma fara bayarwa a wasu jihohi biyar a ranar 28 ga watan nan na Nuwamba.
Daga cikin jihohin da aka kebe za a bayar a ranakun da aka diba akwai jihar Kano da Adamawa da Imo da Lagos da Nasarawa da Plateau da Rivers da dai sauransu.






