Mu muka kashe Sheikh Albani - Shekau

'Yan Boko Haram sun hallaka daruruwan mutane a Nigeria

Asalin hoton, AFP

Bayanan hoto, 'Yan Boko Haram sun hallaka daruruwan mutane a Nigeria

Kungiyar Boko Haram ta yi ikirarin cewar ita ce ta hallaka sanannen Malamin addinnin musulunci na Zaria, Sheikh Mohammed Auwal Adam Albani.

Kungiyar ta bayyana haka ne a cikin wani faifan bidiyo da ta fitar, inda Shugaban kungiyar Abubakar Shekau ya yi jawabi.

An dai kashe Sheikh Albani ne tare da uwargidansa da kuma dansa a wani hari da aka kai musu a Zaria.

Kungiyar ta Boko Haram ta kuma ce ita ce ke da alhakin hare haren baya bayan nan da aka kai musamman a jihar Borno.

A cewar Abubakar Shekau, kungiyar za ta kaddamar da hari kan wasu manyan 'yan siyasa a Nigeria wadanda ke goyon bayan demokradiya.