Yakin Yemen: Joe Biden na son Saudiyya ya kawo karshen yakin da ƴan Houthi

Children play near a building damaged by bombing, Yemen (file pic - November 2018)

Asalin hoton, Reuters

Bayanan hoto, Miliyoyin 'yan Yemen na bukatar abinci da magani da kuma muhalli bayan an shafe shekara shida ana yaki

Amurka za ta kawo karshen goyon bayan da ta ke ba kawayenta da ke yaki a Yemen, kasar da aka daidaita da rikicin shekara shida wanda kuma ya lakume rayuka fiye da 110,000.

"Tilas a kawo ƙarshen yaƙin Yemen," inji shugaban Amurka cikin wani jawabi na alƙiblar da gwamnatinsa za ta fuskanta a fagen dangantakar ta da ƙasashen waje.

A karkashin shugabannin Amurka biyu na baya-bayan nan da ya gada, Amurka ta rika goya wa Saudiyya baya ne a yakin da ta ke yi da 'yan Houthi na Yemen.

Wannan rikicin ya janyo wa miliyoyin 'yan kasar ta Yemen wahalhalu da matsananciyar yunwa.

An dai fara yakin ne a 2014 tsakanin gwamnatin Yemen da kungiyar 'yan tawaye ta 'yan Houthi. Bayan shekara guda rikicin ya kara kazancewa bayan da Saudiyya da kawayenta - kasashen Larabawa takwas - da Amurka ke mara wa baya tare da Birtaniya da Faransa su ka fara kai wa 'yan Houthin hare-hare.

Amma Mista Biden ya sanar da sauyin alkibla a dangantakar Amurka da sauran kasashen duniya, wanda ya hada da wannan matakin na kawo karshen yakin

Kalaman Mista Biden sun yi hannun riga da na mutumin da ya gada - tsohon shugaba Donald Trump wanda ya sauka daga mukaminsa a watan jiya.