Covid-19: Amurka ta soma kwashe 'yan kasarta daga Najeriya

Amurkawa

Asalin hoton, Twitter/@USEmbassyAbuja

Lokacin karatu: Minti 1

Amurka ta soma kwashe 'yan kasarsa daga Najeriya a yayin da duniya ke ci gaba da fama da annobar coronavirus.

Sanarwar da ofishin jakadancin Amurka a Najeriya ya wallafa a shafinsa na Twitter ranar Talata, ya ce tun ranar Litinin aka kwashe Amurkawa 376 daga kasar zuwa birnin Washington.

Kauce wa X
Ya kamata a bar bayanan X?

Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

Gargadi: Ana iya samun talla wanda ba na BBC ba ne

Karshen labarin da aka sa a X

Ofishin ya kara da cewa za a ci gaba da kwashe Amurkawa daga Najeriya zuwa Washington.

A makon jiya Amurka ta sanar cewa za ta soma kwashe 'ya'yanta daga Najeriya, jim kadan bayan Shugaba Muhammadu Buhari ya sanar da rufe jihohin Lagos da Ogun da kuma babban birnin tarayya Abuja.

Karin bayani kan coronavirus
Karin bayani kan coronavirus

Alkaluma dai sun nuna cewa coronavirus ta fi yin illa a Amurka inda ya zuwa ranar Talata mutum fiye da 360, 000 suka kamu da cutar yayin da mutum sama da 10,000 suka mutu.

A Najeriya, alkaluma sun nuna cewa mutum 238 ne suka kamu da cutar yayin da mutum biyar suka mutu.