Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.
Covid-19: Mutum 6 sun sake kamuwa a Najeriya
Hukumar yaki da cututtuka masu yaduwa ta Najeriya NCDC, ta bayyana cewa an samu karin mutum shida da suka kamu da annobar coronavirus a kasar.
NCDC, ta wallafa hakan a shafinta na twitter da misalin karfe 9:30 na daren ranar Litinin 6 ga watan Afrilu cewa an sake samu karin mutanen da ke dauke da cutar.
Hukumar ta ce cikin wadanda suka kamu, 2 a Kwara suke, sai 2 a Edo da 1 a kuma Abuja babban birnin tarayyar kasar sannan 1 kuma a Rivers.
Ya zuwa yanzu dai akwai adadin mutane 238 da aka tabbatar sun kamu da cutar, inda 35 daga cikinsu sun warke, sai kuma 5 da suka rasu a Najeriyar.
A ranar 22 ga watan Maris ne hukumar ta bayar da sanarwar samun mutum na farko da ya mutu sakamakon wannan annoba a kasar.
Jihar Legas ce har yanzu take kan gaba a yawan masu dauke da cutar ta covid-19, kuma adadinsu ya haura 100 ya zuwa yanzu.
Jihohin da cutar ta bulla zuwa yanzu
Legas - 120
Abuja - 48
Osun - 20
Oyo - 9
Edo - 11
Bauchi - 6
Akwa Ibom - 5
Kaduna - 5
Ogun - 4
Enugu - 2
Ekiti - 2
Rivers -2
Benue - 1
Ondo - 1
Kwara- 2
Karin labaran da za ku so ku karanta