Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.
Hotunan hatsarin jirgin ƙasan Abuja zuwa Kaduna
Da safiyar yau Talata ne aka samu wani hatsarin jirgin ƙasan Abuja zuwa Kaduna a yankin arewacin Najeriya.
Jirgin ƙasan ɗauke da fasinja da ya taso daga Abuja babban birnin Najeriya zuwa Kaduna ya goce daga kan layinsa ne, lamarin da ya sa wani ɓangare nasa ya faɗi jim kaɗan bayan ya bar Abuja.
Lamarin ya jefa fargaba a tsakanin fasinjoji da ke cikin jirgin da ma ƴan'uwa da abokan arziki.
Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne a ƙauyen Asham da ke hanyar Abuja zuwa Kaduna.
Har yanzu ba a san abin da ya jawo saukar jirgin daga kan layin dogo ba, kuma babu tabbacin ko an samu waɗanda suka jikkata.
Tuni dai hukumar kula da zirga-zirgar jiragen ƙasa ta Najeriya NRC ta sanar dakatar da jigilar jiragen ƙasa tsakanin Abuja zuwa Kaduna har sai lokacin da aka gyara hanyar.
Shugaban hukumar sufurin jiragen ƙasa ta ƙasar, NRC, Kayode Opeifa, ne ya sanar da hakan yayin da yake zantawa da manema labarai a Abuja, sa'o'i bayan faruwar lamarin.
Opeifa ya ce wasu ma'aikatan hukumar tare da hukumar binciken sufuri ta Najeriya (NSIB) da sauran hukumomin da abin ya shafa, a halin yanzu suna nan a wurin da jirgin ƙasa ya tuntsure suna gudanar da bincike.
Wasu ƴan ƙasar sun alaƙanta hatsarin da rashin kyawu da ingancin jiragen ƙasan.
To sai dai shugaban hukumar sufurin jiragen ƙasar ya yi watsi da iƙirarin.
Shugaban na NRC ya kuma karɓi wasu fasinjojin da ke cikin jirgin a tashar Asham da kuma tashar jirgin ƙasa ta Idu.
Tuni dai shugaban hukumar sufurin jiragen ƙasan ya ce an fara mayar wa fasinjojin da ke cikin jirgin kuɗaɗen tikitinsu