"Mu bar yaudarar kanmu shugabanni mu ne matsalar arewa"
Lokacin karatu: Minti 1
Gwamna Uba Sani na jihar Kaduna ya ce lokaci har yanzu bai ƙure ba, ga shugabanni a arewacin Najeriya da su farka, su tsamo al'ummominsu daga halin fatara da rashin ilmi da ke addabar yankin.
Ya ce duk da yake, masu zanga-zangar yunwa suna da hujjar su fito su nuna fushinsu ga gwamnati, amma masu zugasu don fitowa zanga-zangar, akasari sun riƙe madafun iko a baya, amma suka kasa inganta rayuwar jama'a.
Gwamnan ya bayyana haka ne yayin zantawa da BBC a kan zanga-zangar da aka shiga a faɗin Najeriya da kuma tarzomar da aka samu a wasu jihohi ciki har da jiharsa ta Kaduna.
Ya ce lokaci ya yi da shugabanni a yankin za su faɗa wa kansu gaskiya kuma yana kiran dukkansu 'ciki har da ni a kan mu ji tsoron Allah'








