Zaɓi biyu da suka rage wa PDP gabanin babban zaɓen Najeriya na 2027

Asalin hoton, X/PDP
PDP ita ce babbar jam'iyyar adawa a Najeriya, kuma ɗaya daga cikin mafi daɗewa. Jam'iyyar ce ta mulki Najeriya daga 1999 lokacin da ƙasar ta koma mulkin dimokuraɗiyya har zuwa shekara ta 2015, sai dai rikicin da ke addabar jam'iyyar ta sa ta yi asarar jihohi 31 ga jam'iyyar APC mai mulki.
Jam'iyyar da ya kamata ta zamo barazana, a yanzu tana cikin mawuyacin hali inda ta dare zuwa ɓangarori, hakan ya sanya tana cikin barazana gabanin babban zaɓen ƙasar na 2027.
Yayin da ake faman kai-komo a kotu, yanzu jam'iyyar ta dare zuwa gida biyu, ɗayan ɓangaren na ƙarƙashin gwamnan jihar Oyo Seyi Makinde da na Bauchi Bala Mohammed.
Ɗayan ɓangaren kuma na yin biyayya ga ministan babban birnin Najeriya, Abuja, Nyesom Wike, wanda ya ƙi fita daga jam'iyyar duk da cewa yana riƙe da muƙami a gwamnatin Bola Tinubu ta jam'iyyar APC.
Yanzu akwai kimanin ƙararraki 9 a gaban kotu game da halin da PDP ke ciki. Lamarin ya sanya gwamnonin jam'iyyar da dama suka fice daga cikinta.
A baya-bayan nan ne kotun ɗaukaka ƙara ta sake tabbatar da hukuncin wata ƙaramar kotu kan cewa kada hukumar zaɓen Najeriya ta amince da zaɓen shugabannin jam'iyyar da aka yi a garin Ibadan na jihar Oyo a ranakun 15 da 16 ga watan Nuwamban 2025.
A taron na garin Ibadan ne ƴaƴan jam'iyyar suka zaɓi Tanimu Turaki a matsayin shugaban jam'iyyar na ƙasa da kuma Taofeek Arapaja a matsayin sakataren jam'iyyar na ƙasa, da kuma sauran shugabanni.
A lokacin taron ne jam'iyyar ta kori ministan Abuja Nyesom Wike, da Ayo Fayose da wasu manyan jam'iyyar bisa zargin su da ayyukan zagon-ƙasa.
Wasu masu ruwa da tsaki a jam'iyyar sun buƙaci ɓangaren Tanimu Turaki ya amshi hukuncin kotun ɗaukaka ƙara na baya-bayan nan, tare da sulhuntawa da ɓarin Nyesom Wike, ta yadda jam'iyyar za ta sake yin wani babban taro, kasancewar wasu na tsoron cewa hukumar zaɓen Najeriya ta INEC na iya haramta mata fitar da ƴan takara a zaɓen 2027 idan rikicin ya ci gaba.
Yayin da jam'iyyar ke fama da wannan rikice-rikice, jadawalin hukumar zaɓe ya nuna cewa jam'iyyu za su yi zaɓen fitar da gwani ne tsakanin 23 ga watan Afrilu zuwa 30 ga watan Mayun wannan shekara ta 2026.
Wane zaɓi ya rage wa PDP kafin zaɓen 2027?

Asalin hoton, Olukayode Jaiyeola/NurPhoto via Getty Images
Yanzu za ku iya samun labaran BBC Hausa kai-tsaye a wayoyinku.
Latsa nan domin shiga
Karshen Whatsapp
Wasu ƴaƴan jam'iyyar na ganin cewa ya kamata a janye duk wasu ƙararraki da ke gaban kotu game da rikicin shugabancin jam'iyyar.
Tsohon shugaban majalisar dattijan Najeriya, Bukola Saraki ya roƙi jagororin jam'iyyar da masu ruwa da tsaki su jefar da makaman yaƙinsu, su sake tsara wani babban taron ƙasa wanda zai yi daidai da dokokin hukumar zaɓe.
"Matsayata ita ce kotun ƙoli ta riga ta yanke hukunci. amma idan muka lura da jadawalin zaɓen 2027 da hukumar INEC ta fitar, a bayyane yake cewa babu lokacin da za mu jira hukuncin kotun ƙoli."
Saraki ya ce idan har ba a warware matsalar jam'iyyar ba, PDP ba za ta iya fitar da ƴan takara ba domin zaɓen 2027.
Ya ce ya kamata jam'iyyar ta mayar da hankali kan gyara kanta a maimakon ɗaukaka ƙarar zuwa kotun ƙoli.
"Na yi amannar cewa hanya ɗaya da muke da ita, ita ce mu janye duk wasu ƙararraki mu yi amfani da tsarin da muke da shi a yanzu, mu gudanar da babban taron ƙasa daidai da jadawalin hukumar zaɓe."
Saraki ya ce shugabannin jam'iyyar waɗanda ba su samu yadda suke so ba daga ƙararrakin da suka shigar a kotu, ya kamata su yi la'akari da 'abin da zai fi dacewa ga jam'iyyar ta PDP a zaɓen 2027 da kuma bayan hakan.'
Saraki ya ce akwai ƴaƴan jam'iyyar da ke son yin takara a zaɓen 2027 ƙarƙashin lemar jam'iyyar, saboda haka wannan lokaci ne da ya kamata a taimaka musu.
A wani ɓangaren kuma, sanata mai wakiltar mazaɓar Kogi ta tsakiya a majalisar dattijan Najeriya, Natasha Akpoti Uduaghan, ita ma ta yi tsokaci kan rikicin na PDP.
Ta ce ya kamata dukkanin ɓangarorin su sasanta da juna sannan su manta da batun ƙararraki a kotu.
Ta ce 'lokaci ne na ƙoƙarin ƙarfafa dimokuradiyya a cikin gida' gabanin babban zaɓen 2027.
Ta ce ci gaba da jan ƙararraki a kotu ba zai fitar da jam'iyyar ba, kuma hakan ba zai yi wa masu son yin takara ƙarƙashin jam'iyyar amfani ba.
"A lokaci irin wannan, ya kamata mu yi watsi da son rai, mu mayar da hankali kan abin da zai amfani jam'iyyarmu da ƙasar baki ɗaya," in ji Natasha.
Masana siyasa na ganin cewa zaɓi biyu da suka rage wa jam'iyyar su ne: ko dai duka ɓangarorin biyu su sulhunta, su watsar da bambance-bambancen da ke tsakaninsu ko kuma babu tabbas kan halin da jam'iyyar za ta faɗa idan ta ci gaba da bibiyar ƙararrakin da aka shigar a kotu.
Jerin jihohin da APC ke mulki da kuma na PDP

Asalin hoton, Uno Emo/X, Peter Mbah/X, Duoye Diri/X, Sheriff Oborevwori/X
Abia - Alex Otti - Labour Party
Adamawa - Ahmadu Umaru Fintiri - APC
Akwa Ibom - Umo Eno - APC
Anambra - Charles Soludo - APGA
Bauchi State - Bala Muhammed- PDP
Bayelsa - Douye Diri - APC
Benue - Hyacinth Alia - APC
Borno - Babagana Zulum - APC
Cross River - Bassey Otu - APC
Delta - Sheriff Oborevwori - APC
Ebonyi - Francis Nwifuru - APC
Edo - Monday Okpebholo- APC
Ekiti - Biodun Oyebanji - APC
Enugu - Peter Mbah -APC
Gombe - Muhammad Inuwa Yahaya - APC
Imo - Hope Uzodinma -APC
Jigawa - Umar Namadi - APC
Kaduna - Uba Sani - APC
Kano - Abba Kabir Yusuf - APC
Katsina - Dikko Umaru Radda - APC
Kebbi - Nasir Idris - APC
Kogi - Ahmed Usman Ododo - APC
Kwara - AbdulRahman AbdulRazaq - APC
Lagos - Babajide Sanwo-Olu - APC
Nasarawa - Abdullahi Sule - APC
Niger - Mohammed Umar Bago - APC
Ogun - Dapo Abiodun - APC
Ondo - Lucky Aiyedatiwa - APC
Osun - Ademola Adeleke - Accord Party
Oyo - Seyi Makinde - PDP
Plateau - Caleb Mutfwang - APC
Rivers - Siminalayi Fubara - APC
Sokoto - Ahmad Aliyu - APC
Taraba - Agbu Kefas - APC
Yobe - Mai Mala Buni - APC
Zamfara - Dauda Lawal - APC
FCT: Nyesome Wike







