Karawar karshe tsakanin Dino da Adeyemi

BBC
Lokacin karatu: Minti 1

A ranar Asabar 30 ga watan Nuwamba ne ake gudanar da karashen zabe zagaye na biyu na kujerar dan majalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta yamma.

'Yan takarar sun hada da Dino Melaye na jam'iyyar PDP da kuma Smart Adeyemi na jam'iyyar APC.

Bayan zaben da aka gudanar a ranar 16 ga watan Nuwamba, hukumar INEC ta bayyana zaben a matsayin wanda bai kammalu ba (inconclusive.)

A wannan karon za a gudanar da karashen zaben a rumfuna 53.

Ana sa ran cewa masu zabe 45,767 ne za su kada kuri'a daga kananan hukumomi bakwai a fadin jihar.

@inecnigeria

Asalin hoton, @inecnigeria

A zaben da aka gudanar ranar 16 ga watan Nuwamba, hukumar zabe a jihar ta bayyana cewa zaben bai kammalu ba kasancewar kuri'un da aka soke sunfi yawan wadanda wanda ke kan gaba ya bada tazara.

Smart Adeyemi na jam'iyyar APC ke kan gaba da kuri'u 80,118, yayin da mai bin sa Dino Melaye na jam'iyyar PDP ke da kuri'u 59,548.

Hukumar zaben Najeriya INEC a shafinta na twitter ta bayyana cewa tuni aka fara gudanar da zaben a wasu kananan hukumomi a fadin jihar ta Kogi.

Kauce wa X
Ya kamata a bar bayanan X?

Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

Gargadi: Ana iya samun talla wanda ba na BBC ba ne

Karshen labarin da aka sa a X

A kwanakin baya ne dai kotun sauraron kararrakin zabe ta garin Lokoja da ke jihar Kogi ce ta soke zaben Sanata Dino Melaye, wanda yake wakiltar shiyyar Kogi ta Yamma a Majalisar Dattawan Najeriya.