Gwamnatin Somalia ta yanke hulɗa da Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa
Gwamnatin Somaliya ta sanar da yanke hulda da Hadaddiyar Daular Larabawa, tare da soke duk wasu yarjejeniyoyin da aka kulla tsakanin ƙasashen biyu.
Wata sanarwa da aka fitar bayan taron majalisar ministocin ƙasar ta ce an soke duk wasu yarjejeniyoyin da aka rattabawa hannu da Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa da suka haɗa da tasoshin jiragen ruwa da haɗin gwiwar tsaro.
Matakin ya shafi duk shirye-shiryen da suka shafi tashoshin jiragen ruwa a Berbera, Bosaaso, da Kismayo, da kuma yarjejeniyoyin da aka yi da hukumomin tarayya, da hukumomin da ke da alaƙa da su, da kuma gwamnatocin yankuna.
Daga cikin yarjejeniyoyin da abin ya shafa har da yarjejeniyar tashar jiragen ruwa ta Berbera, wadda a ƙarƙashinta gwamnatin Somaliland ta rattaba hannu a kan yarjejeniyar gudanarwa a shekarar 2016 da kamfanin DP World.
Gwamnatin Somaliya dai ta daɗe tana adawa da yarjejeniyar, tana mai cewa an ƙulla yarjejeniyar ba tare da amincewar gwamnatin tarayya ba.
Gwamnatin ta ce an ɗauki matakin ne domin kare ƴancin Somaliya da haɗin kan yankunan ƙasar, da kuma tsarin mulkinta.






















