Wasan sada zumunta: Karon farko da Najeriya za ta kara da Tunisia tun bayan kofin Afirka

Nigeria vs Tunisia

Asalin hoton, Getty Images

Tawagar kwallon kafa ta Najeria za ta buga wasan sada zumunta da ta Tunisia ranar Talata a Austria.

Wannan ne wasa na biyu da Najeriya za ta buga tun bayan wata 11 da ta je ta doke Lesotho da ci 4-2 a karawar neman shiga gasar cin kofin nahiyar Afirka.

A ranar Juma'a Algeria mai rike da kofin nahiyar Afirka ta doke Super Eagles da ci 1-0 a wasan sada zumunta da suka kara a Austria.

Super Eagles na buga wasannin ne don shirin tunkarar karawa da Saliyo a cikin watan Nuwambar 2020 a fafatawar neman gurbin shiga gasar cin kofin nahiyar Afirka.

Ramy Bensebaini ne ya ci Algeria kwallon da ya bai wa koci Djamel Belmadi dama ta biyu da ya yi nasara a kan Najeria har da ta gasar cin kofin nahiyar Afirka da suka kara a Masar.

Nigeria ta yi nasara a kan Tunisia da ci 1-0 a wasan neman mataki na uku da suka fafata a Cairo a 2019, kuma Odion Ighalo ne ya ci wa Super Eagles kwallon.

Wasu wasannin sada zumunta da za a buga ranar Talata:

  • Japan da Ivory Coast
  • Morocco da Jamhuriyar Dumukaradiyyar Congo
  • Mexico da Algeria