'Yan mata 11 aka sace a kauyukan Gwoza

Rahotanni daga jihar Borno na cewar adadin 'yan matan da 'yan Boko Haram suka sace a kauyukan Gwoza ya kai goma sha daya.
Mazauna kauyen Warabe sun tabbatarwa BBC cewar an sace 'yan mata takwas a kauyensu a ranar Lahadi.
Sai dai kuma kamfanin dillancin labarai na AFP ya ruwaito cewar an sace karin wasu 'yan matan uku a kauyen Wala da ke makwabtaka da Warabe.
Shugaban Boko Haram, Abubakar Shekau ya ce kungiyarsa ce ta sace 'yan mata 276 a garin Chibok a ranar 14 ga watan Afrilu kuma ya yi barazanar 'sayar da su a kasuwa'.
Jihar Borno ta kasance matattarar 'yan Boko Haram kuma yankin Gwoza na yawan fuskantar hare-hare daga wajen 'yan Boko Haram.
Amurka ta ce za ta taimaka wa Nigeria wajen neman 'yan matan Chibok.
Shugaba Obama ya ce za a tura tawaga, da ta kunshi sojoji da jami'an tsaro da kuma jami'an wasu hukomomi wadanda za su yi kokarin gano takamammen wurin da aka ajiye 'yan matan.







