Bayanan hoto, Duk da yanayin tsaro ya inganta a arewa maso gabashi - amma har yanzu mutane da yawa ba za su koma ba.
Yayin da Shugaba Muhammadu Buhari ke neman takarar shugabancin Najeriya shekara takwas baya, ya zo da alƙawarin cewa zai taimaka wajen kawo karshen matsalar Boko Haram wanda ya tilastawa Miliyoyin mutane barin muhallansu daga arewa maso gabashin ƙasar zuwa wasu yankuna.
Yanzu shekara takwas kenan da wannan alƙawarin kuma yanzu ya samu zaman lafiya, kuma an kwato wasu yankuna masu girma wanda a baya mayaƙan Boko Haram suka ce sun ƙwace su. Sai dai yayin da 'yan Najeriya ke ƙoƙarin zaɓar magajinsa, halin da ake ciki cike yake da ru ɗani.
Ruƙayya Goni wadda ke zaune kusa da wata makarantar firaimare da masu iƙirarin jihadin suka ƙona, lokacin da suka ƙwace yankin Damasak a ƙarshen 2014.
Manufar Boko Haram dai ita ce "ilimin boko haramun ne" kungiyar ta sha kai hare-harenta kan makarantun da babu ruwansu da addini, tare da sace sama da 'yan makaranta 200 daga garin Chibok.
Shekara tara da ta gabata, Ruƙayya ta gudu daga gidanta tare da iyalanta su 11, inda suka tsallaka iyakar da take kusa da su ta ƙasar Nijar.
"Mun gudu ne saboda matsalar tsaro da Boko Haram ta janyo" ta bayyana da yaren Kanuri, kuma wani mai fassara ya fassara. "Sun kwace Damasak shi yasa muka tsallaka Diffa, da ke Nijar." A lokacin tana da 'yarta 'yar shekara shida da haihuwa. Ta haifi duka 'ya'yanta maza biyar a Nijar daga baya kuma ta koma Damasak a bara.
"Mun ji cewa komai ya daidaita a yanzu, shi yasa muka yanke shawarar mu koma gida," kamar yadda ta yi bayani. Na tambayeta ko ta taɓa tunanin komowa gida. "Eh muna ta fatan komawa gida, kullum sai mun yi addu'ar zaman lafiya. Na ji daɗin koma. Babu wani wuri da ya fi gida.
Asalin hoton, Kyla Herrmannsen/ BBC
Bayanan hoto, Rukaiya Goni na zaune ne a Nijar da ke maƙwaɓtaka da Najeriya na tsawo shekaru, amma a ƙarshe ta koma Damasak inda gida ne a gareta.
Duk lokacin da aka tambayi Shugaba Buhari da magoya bayansa game da tsaron yankin sai su ce, yanayin tsaro ya fi na lokacin baya da suka karɓi mulki.
Idan aka yi la'akari da mutane irinsu Ruƙayya da suka koma gida za ka iya cewa iƙirarunsu na kan daidai. Sai dai har yanzu saman lafiya ya yi wa yankin nisa.
"Matsalar tsaro har yanzu na kaikawo a yankin, kuma mafi mahimmanci shi ne yana shafar mutanen da suke nan domin taimakawa," in ji David Stevenson, daraktan hukumar abinci ta duniya a Najeriya.
"Suna ci gaba da tserewa, akwai sabbin da suka zo amma suna shaida mana ba sa jin cewa suna da aminci a nan ko a wuraren nomansu."
Kungiyoyin masu iƙirarin jihadi irinsu Boko Haram, har yanzu suna da barazana kan tsaro a Borno duk da cewa ba su da yankuna da yawa a ƙarƙashinsu.
Akwai yankunan jihar da dama da ake ganin suna da haɗari idan za a shige su a mota. Idan har kana son zaman lafiya daga Damaturu da ke Yobe zuwa Maiduguri babban birnin Borno sai dai ka tafi a jirgin saman MDD.
Kungiyar ISWAP da ta ɓalle daga Boko Haram shkaru bakwai baya, ita ma na ƙara zama babbar barazana. A 2022 ta yi iƙirarin kai hare-hare sama da na kowacce ƙungiya tun bayan kafata, kuma a nitse ta kama yankin Tafkin Chadi mai mahimmanci.
Akwai bayanai da ke cewa ayyukan ƙungiyar sun fara tsallakawa yankin arewa maso yammacin ƙasar, inda suka haɗa kai da gungun masu satar mutane.
Kundin tsarin mulkin Najeriya ya haramtawa Buhari sake takara, amma rashin kakkaɓe matsalar tsaron da ke addabar ƙasar da kuma yadda matsalar ke yaɗo ya sanya mutane a arewacin Najeriya sanya ayar tamabaya a kan jam'iyyarsa ta APC.
A jihar Kano ɗaya daga cikin manyan garuruwan kasuwanci a yankin Afrika ta Yamma, wani ɗan kasuwa Muktar Garba Intini ya ce ba zai zaɓi APC ba.
Asalin hoton, Kyla Herrmannsen/ BBC
Bayanan hoto, Mukhtar Garba Intini baya son APC ta ci mulki
"Ƙarƙashin mulkin APC mun sha wuya, shi yasa muke addu'a PDP ta dawo," in ji Malam Intini. Yana siyo hatsin da yake kasuwancinsa ne daga Maiduguri, ko da yaushe cikin fargabar matsalar tsaro yake.
"Rashin tsaro matsala ne, akwai mutanenmu da yawa da suka tafi Maiduguri har yanzu ba ma jin ɗuriyarsu, kullum addu'a muke musu."
Rashin tsaron wani abu ne da matafiya a kullum ke fuskanta. Duk lokacin da muke tafiyar kilomita 300 daga gabashin zuwa Potiskum a Yobe, sai dai mu yi amfani da mota mai sulke, tun da masu garkuwa da mutane sun mamaye titinan namu.
Asalin hoton, Kyla Herrmannsen/ BBC
Bayanan hoto, A iya cewa an ci ƙarfin Boko Haram, amma tasirinsu har yanzu yana nan a yankin
Gazawar Buhari wajen magance matsalar tsaro shi ne dalilin da magoya bayan Atiku Abubakar na jam'iyyar PDP mai adawa suke ganin ya kamata a ba shi wannan damar a wannan karon. Ganin cewa shi kaɗai ne ɗan takarar da ya fito daga yankin.
Dolly Kola-Balogun 'yar ksuwa ce kuma magoyin bayan PDP da ke zaune a Abuja babban birnin Najeriya.
"Ba na goyon APC saboda sun kasa a ganina a mataki na ƙasa. Sun kasa kawo ƙarshen rashin tsaro a arewa maso gabas, kuma yanzu ga matsalar garkuwa da mutane domin karɓar kuɗin fansa.
Tana ganin mutanen da suka yi rijistar zaɓe da niyyar zaɓen suna da yawa, duk da cewa ya girmi duka 'yan takarar da ce neman shugabancin ƙasar, ya kai shekara 76. Kimanin kashi 40 cikin miliyan goma sabbin masu rijistar matasa na 'yan ƙasa da shekara 35 ne, kuma kusan duka Atiku suke so.
Zaben Najeriya 2023: Waɗanne alƙawura ne jam'iyyu suka yi muku
Tsare tsaren Jam'iyyu
All Progressives Congress
Manyan muradu
Bunƙasa fitar da kaya daga Najeriya da kuma rage dogaro kan shigo da kaya
Rage adadin matasa marasa aikin yi da kashi hamsin cikin ɗari a cikin shekara huɗu da kuma samar da ayyuka miliyan ɗaya a ɓangaren sadarwa na zamani.
Ɗaukar matakan tabbatar da cin gashin kan ɓangaren shari'a ta fannin kuɗi da gudanarwa.
Tattalin arziki
Tallafa wa masana'antun cikin gida ta hanyar sauƙaƙa musu kuɗin haraji.
Kula da farashin kaya domin rage hauhawar farashi
Cire tallafi kan gas cikin wata shida da kuma ƙara yawan gas ɗin da ake samarwa da kashi 20%.
Aikin yi
Samar da ayyuka miliyan guda ta ɓangaren sadarwar zamani a cikin watanni 24 na farkon gwamnati.
Rage adadin matasa marasa aikin yi da kashi hamsin cikin ɗari a cikin shekara huɗu.
Tallafa wa masu sana'a miliyan biyu da kuma ƙwararru domin horas da matasa hanyoyin samun aiki da fara kasuwanci.
Kiwon lafiya
Aiwatar da shirin inshorar lafiya na tilas wanda kashi 40 cikin 100 na jama'a za su amfana a cikin shekara biyu.
Ƙara adadi da kuma inganta ma'aikatan lafiya musamman waɗanda suke aiki a matakin farko.
Aiki tare da gwamnatin jihohi da ƙananan hukumomi don samar da asibitocin tafi da gidanka domin tabbatar da cewa kowa na da asibiti aƙalla kilomita uku a kusa ko kuma tafiyar minti 30.
Ƙarfafa gwiwa don samar da magunguna da rigakafi a cikin Najeriya.
Tsaro
Ƙara Inganta albashi da walwalar ma'aikatan tsaro da kuma samar da wani shiri na musamman domin bayar da alawus ga sojoji da suka samu rauni da kuma waɗanda suka rasu a kan aiki.
Samar da makamai masu inganci, da inganta ɓangaren sadarwa da sufuri a sansanonin sojoji.
Ƙara dauka da horas da sabbin ma'aikatan soji da ƴan sanda da jami'an tsaron sirri da sauran masu kayan sarki.
Kawar da kai hare-hare kan muhimman wurare na gwamnati
Ilimi
Samar da sabbin hanyoyin tantance ingancin duka cibiyoyin ilimi tun daga firamare har zuwa jami'a.
Samar da shirin gwaji na bayar da bashi ga ɗalibai.
Samar da wani asusun ɗalibai na musamman wanda babu lamunin gwamnati a ciki.
Cin hanci da rashawa
Ƙayyade adadin kuɗaɗen da za a iya kashewa kan samar da gine-ginen gwamnati da albashi da kuma kan zaɓaɓɓun shugabanni da ma'aikatan gwamnati.
Ƙara samar da haraji ta hanyar rage kuɗaɗen da suke zurarewa daga ɓangaren kuɗin.
Saka wa masu aiki tuƙuru da kawar da ayyuka da ma'aikatan bogi.
Kawo sauyi ɓangaren aikin gwamnati domin rage abubuwan da ke kawo cikas, ko rashin ingancin aiki, da kuma ɓarna.
Labour Party
Manyan muradu
Gudanar da sauye-sauye a aikin gwamnati da ɓangaren shari'a domin tabbatar da bin doka, da yaƙi da rashawa da kuma tsimin kuɗi wurin tafiyar da gwamnati.
Mayar da Najeriya ƙasar da ke sana'anta abubuwan buƙata a maimakon sayowa daga wasu ƙasashe.
Fifita bunƙasa al'umma ta hanyar zuba jari a ɓangaren ilimin kimiyya da lafiya, abubuwan kawo ci gaba.
Tattalin arziki
Ɗora tattalin arziƙin Najeriya a kan tafarkin ƙirƙira da samar da kamfanoni ta yadda ƙasar za ta rinƙa fitar da kaya zuwa waje.
Rage tashin farashin kaya, da tabbatar da cin gashin kai na babban bankin ƙasar, da kyautata tsarin biyan haraji.
Rage dogaron da Najeriya ke yi kan man fetur ta hanyar inganta ɓangaren masana'antu.
Sassauta takunkumi kan kayan da ake shigowa da su daga ƙasashen waje da canjin kuɗi, tare kuma da samar da tsarin musayar kuɗi guda ɗaya.
Aikin yi
Faɗaɗa hanyoyin samar da kuɗi ga ƙanana da matsakaitan sana'o'i, da mata da matasa domin rage matsalar rashin aikin yi.
Zuba jari a ɓangaren bunƙasa al'umma.
Inganta hanyar sauƙaƙa yin kasuwanci a ƙasar domin janyo masu zuba jari ta yadda za a samar da kamfanoni.
Samar da yanayi mai kyau na bunƙasar ƙananan sana'o'i.
Kiwon lafiya
Inganta albashi da kuma yanayin aikin ma'aikatan lafiya.
Samar da inshorar lafiya ga talakawan Najeriya miliyan 133, musamman mata masu ciki, da yara, da tsofaffi da kuma masu lalurar nakasa.
Ƙara wa malaman lafiya ilimi ta hanyar bayar da horo.
Samar da kiwon lafiya mai sauƙi ga kowa.
Tsaro
Kawo ƙarshen ayyukan ƴan bindiga da na masu tayar da ƙayar baya.
Haɗa kai da ƙasashen yammaci da na tsakiyar nahiyar Afirka domin inganta tsaro na kan iyaka, musamman ƙasashen Chadi da Jamhuriyar Nijar, da Kamaru.
Haɗa hannu da majalisar dokoki domin samar da jami'an tsaro na cikin al'umma.
Ƙara yawan jami'an soji, da ƴan sanda da sauran hukumomin tsaro, da samar masu da kayan aiki, da ba su horaswa, da samar masu da kuɗaɗe ta yadda za su iya magance barazanar tsaro.
Ilimi
Zuba jari a ɓangaren koyar da sana'o'i, da wasannin motsa jiki, da horaswa kan ilimin fasahar zamani daga makarantun firamare zuwa sakandare.
Tsarin ilimi wanda 'ba za a bar kowane yaro a baya ba'
Samar da tsarin biyan harajin kamfanoni ta hanyar kula da makarantu mallakin gwamnati, samar da tsarin karatu da kula da ayyukansu.
Ware kashi 14% na kasafin kuɗi ga ɓangaren ilimi.
Cin hanci da rashawa
Yin biyayya ga dokoki na tsarin kuɗi.
Binciken harkokin kuɗi na kowane fallen gwamnati a kai-a kai
Toshe duk wasu hanyoyin zurarewar kuɗi da kawo ƙarshen tallafin man fetur.
Tafiyar da lamurran gwamnati a bayyane.
New Nigeria Peoples Party
Manyan muradu
Samar da ayyukan yi ta hanyar bunƙasa noma.
Magance matsalar tsao.
Martaba doka da bin ƙa'ida.
Tattalin arziki
Yaƙi da rashawa a ma'aikatu da hukumomin gwamnati domin bunƙasa kuɗaɗen shiga.
Kawo sauyi a kasuwar hannayen jari ta ƙasar domin inganta ta ta yadda za ta zamo hanyar samun kuɗaɗen kasuwanci.
Neman ingantacciyar hanyar tafiyar da kasuwar musayar kuɗi.
Aikin yi
Zaftare yawan marasa aikin yi.
Ƙarfafa wa matasa gwiwa domin shiga harkar noma.
Ƙarfafa wa ɓangaren ƴan kasuwa gwiwa domin su kafa kamfanonin sarrafa amfanin gona domin samar da aikin yi ga matasa.
Kiwon lafiya
Kawo sauyi a shirin inshorar lafiya na ƙasa.
Rage yawan tafiye-tafiye zuwa ƙasashen waje domin neman lafiya, ta hanyar bunƙasa asibitoci, da bunƙasa yadda ake gudanar da aiki, da bayar da horo ga ma'aikatan lafiya.
Samar da ƙarin kuɗi ga ɓangaren kiwon lafiya a cikin kasafin kuɗi.
Tsaro
Samar da isassun kayan aiki da tattara bayanan sirri domin magance matsalar tsaro.
Bunƙasa fahimtar juna da yafiya a tsakanin al'umma.
Yi wa al'umma cikakken bayani kan ayyukan gwamnati.
Ilimi
Samar da isassun kuɗi ga ɓangaren ilimi.
Bunƙasa manyan makarantu kafin samar da sabbi.
Tallafa wa ƙananan hukumomi domin su iya samar da muhalli ga yara sama da miliyan 20 waɗanda ba su zuwa makaranta kuma suke yawo kan titi.
Cin hanci da rashawa
Sauyawa da ƙarfafa hukumomin yaƙi da rashawa.
Tafiyar da ayyukan gwamnati cikin adalci.
Amfani da fasahar zamani domin daƙile ayyukan rashawa.
Peoples Democratic Party
Manyan muradu
Bai wa masana'antu masu zaman kansu fifiko wurin haɓɓaka tattalin arziki.
Ƙara haɗa kan ƴan ƙasa ta hanyar yin raba-dai-dai tsakanin yankunan ƙasar a wurin bayar da muƙamai.
Sauya fasalin gwamnatin Najeriya
Tattalin arziki
Tabbatar da cewa Najeriya ta ci gaba da zama giwar Afrika da tabbatar da cewa ma'aunin GDP ya ruɓanya zuwa $5,000 zuwa 2030.
Haɓɓaka zuba jari ta ɓangaren ababen more rayuwa zuwa kaso 50 na ma'aunin GDP zuwa 2027, kaso 70 kuma zuwa 2023.
Ƙara yawan man fetur ɗin da ake tacewa zuwa ganga miliyan biyu a rana zuwa 2027.
Aikin yi
Samar da ayyukan yi miliyan uku da tsamo mutum miliyan goma daga talauci a duk shekara.
Ƙaddamar da shiri na musamman ingantacce mai rahusa kuma mai dorewa domin samar da aikin yi da kuma sana'o'i.
Samar da wuraren horaswa ga matsakaita da manyan masu sana'o'i.
Kiwon lafiya
Ƙara hanzarta shirin Najeriya na samar da ingantaccen kiwon lafiya kuma mai sauƙi zuwa 2030.
Jawo hankalin likitocin Najeriya da ke ƙasashen waje su dawo gida.
Ƙarfafa gwiwar matsakaita da manyan kamfanonin samar da magunguna da su ƙara adadin magungunan da suke samarwa na cikin gida da ake nema.
Tsaro
Haɓɓaka rajistar haihuwa domin rage aikata laifuka da kuma kare ƴan Najeriya.
Ɗaukar jami'an ƴan sanda miliyan ɗaya domin cimma muradun MDD na kowane mutum 450 ɗan sanda 1.
Ƙara yauƙaƙa dangantaka tsakanin farar hula da sojoji.
Sauya fasalin cibiyoyin tsaro.
Ilimi
Ƙara haɓɓaka karatun kimiyya da fasaha domin samar da dabaru ga sabon tattalin arziki.
Samar da wata hukuma wadda za ta sa ido kan manyan makarantu.
Ƙara zuba jari ta ɓangaren ababen more rayuwa na gwamnatin tarayya da kuma jihohi.
Cin hanci da rashawa
Sake bitar tsarin saka wa ma'aikatan gwamnati masu ƙwazo.
Zamanantar da ayyukan gwamnati domin gano cin hanci.
Tabbatar da cewa hukumomin da suka dace sun aiwatar da hukunci da ake yankewa kan laifukan rashawa.
End of Zaben Najeriya 2023: Waɗanne alƙawura ne jam'iyyu suka yi muku
Mutum miliyan 49 ne suka yi rijistar zaɓe, kuma kusan rabinsu suna zaune ne a yankin arewacin Najeriya, kamar yadda aka saba kuma masu fitowa su yi zaɓe a yankin sun fi yawa idan aka kwatanta da garuruwan da suke kudancin ƙasar kamar su Legas. Kuma idan mutum iya cin yankin za a iya sa masa ran lashe zaɓe.
Wani koma bayan da APC za ta sake fuskanta shi ne mutum miliyan 1.6 da ke gudun hijira a Borno, saboda yaƙin Boko Haram.
Asalin hoton, Ayo Bello/ BBC
Bayanan hoto, Sama da mutum miliyan ɗaya ne ke gudun hijir a Borno
Hauwa Goni tana da shekara 25 a duniya, ta kuma bar ƙauyensu na Dikwa da ke Borno shekara bakwai baya. "Boko Haram sun riƙa kashe mazajen mutane tare da sace wasu da yawa, shi ya sa na yanke shawarar na gudu tare da mijina." Kamar yadda ta yi bayani.
Bayan ta ɗan zauna a Maiduguri sai ya yi ƙoƙarin koma Laegas ɗaya daga cikin manyan biranen ƙasar mafi girma tana da fatan samun rayuwa mai kyau, amma shekara ɗaya kawai ta iya zama.
"Rayuwar ta tsauri da yawa, ga tsada, ba za mu iya ci gaba da zama ba a nan". In ji Hauwa.
Yanzu ta koma Maiduguri, amma an daina kai kayan agaji sansanin da suke, wannan wani mataki ne da gwamnatin APC mai mulki a jihar ta ɗauka domin karfafa gwiwar 'yan gudun hijira domin su koma gidajensu.
Asalin hoton, Ayo Bello/ BBC
Bayanan hoto, 'Yar Hawa Goni na da wata tara da haihuwa a yanzu kuma tana fama da cutar tamowa
Babu ko ɗaya da kai tsaye ya lissafa Boko Haram ko Iswap a cikin manufofinsa. Sun fi magana kan yadda za su kawo ƙarshen masu iƙirarin jihadi baki ɗaya.
Ɗan takarar jam'iyyar APC Bola Tinubu ya ce yana son ƙirƙirar "wata tawaga da za a bai wa horo da kuma tawagar yaƙi da 'yan ta'adda da dakaru na musamman." Domin neman goyon bayan mutanen da wannan bala'i ya shafa ya ce zai smar musu da taimakon gaggawa da na bangare tattalin arziki.
Atiku Abubakar yace zai kawo ƙarshen wannan matsala ta hanyar amfani da wani zaɓi na daban domin warware rikicin ta hanyar diflomasiyya, leƙen asiri, karɓe iko da iyakoki amfani da tsarikan al'ada da kuma haɗa hannu da makotan ƙasashe." Kuma yana so ya kai ci gaba yankin arewa maso gabas.
Shi ma haka ɗan takarar jam'iyyar Labour Peter Obi ya yi maganar zai nemi haɗin kan yankin domin ƙarfafa tsaron kan iyaka, da kuma " gabatar da masu aikata laifuka da 'yan bidiga da 'yan ta'adda wanda hakan zai iya kawo ƙarshen masu aikata laifi ba tare da an hukunta su ba".
Babu wanda ya yi bayanin nawa hakan zai iya laƙumewa a hukumance ko kuma ta yaya za su samo kuɗin yin aikin.
Amma ko wanene ya gaji Buhari na da buƙatar shiri na gaske domin tabbatar da alƙawarin da ya yi shekara takwas baya.