Ba zan kalubalanci cire ni daga sarauta ba – Sarki Sanusi

Asalin hoton, @MSII_dynasty
Tsohon sarkin Kano Muhammadu Sanusi na II ya ce ya riga ya yi gaba ba zai kalubalanci cire shi da gwamnatin Kano ta yi daga sarauta ba.
Sanusi wanda aka dauke shi a wani gajeren bidiyo yana magana da wasu mutane cikin harshen Turanci bayan isarsa Lagos, ya ce da zai je kotu da ya samu nasara saboda wasikar da gwamnatin ta rubuta cike ta ke da kura-kurai.
"Kwata-kwata hujjojin da aka bayar a wasikar ba a rubuta su da kyau ba, abu ne mai sauki in tafi kotu in samu nasara idan ka duba abin da ke cikin wasikar," in ji shi.
"Kotu za ta yi tambayoyi kamar haka; Shin kun tuntube shi? Kun nemi jin ta bakinsa? Kun ba shi dama ya kare kansa? Idan amsoshin a'a ne, shi ke nan za a sami nasara.
"Amma ba zan je kotu ba, gara in fuskanci rayuwa ta gaba kuma."
Ina Muhammadu Sansusi II yake yanzu?

Asalin hoton, @GovKaduna
Da yammacin ranar Juma'a ne tsohon Sarki Sanusi ya bar kauyen Awe na Jihar Nasarawa tare da rakiyar gwamnan Kaduna Malam Nasir El-Rufai.
El-Rufai wanda abokin tsohon sarkin ne, ya raka shi har kofar jirgin da ya shiga zuwa Legas a Abuja.
Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.
Karshen labarin da aka sa a X
Tun farko dai kauyen Loko aka kai shi a Jihar ta Nasarawa, inda ya wayi garin Talata a can.
A ranar Juma'a kuma wata Babbar Kotun Tarayya a Abuja ta bayar da umarnin bai wa tsohon Sarkin na Kano damar shiga ko ina a Najeriya ban da Jihar Kano.
Lauyoyin tsohon sarkin ne suka shigar da kara suna kalubalantar abin da suka kira tauye masa hakkin walwala da kundin tsarin mulki ya ba shi bayan da aka tsare shi a kauyen Loko kafin a mayar da shi garin Awe a Jihar Nasarawa daga baya.

Asalin hoton, @GovKaduna
Hotunan da gwamnatin Jihar Kaduna ta wallafa a shafinta na Twitter ranar Juma'a sun nuna yadda gwamna El-Rufai ya raka tsohon sarki Sanusi har kofar jirgin da ya hau zuwa Legas.










