Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 14/01/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Laraba, 14 ga watan Janairun 2026.

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida, Haruna Kakangi da Ahmad Bawage

  1. Rufewa

    Karshen rahotannin kenan a wannan shafi na labarai kai-tsaye.

    Sai kuma gobe da safe idan Allah ya kai mu.

    Mu kwana lafiya.

  2. Amurka za ta dakatar da bayar da bizar ƴan ci-rani ga ƙasashe 75

    Trump

    Asalin hoton, Getty Images

    Fadar White House ta ce Amurka za ta dakatar da bayar da bizar ƴan ci rani ga ƴan kasashe 75.

    Ƙasashen da hakan ya shafa sun haɗa da Rasha da Iran da Afghanistan da wasu ƙasashen Afirka, har da Thailand da Brazil.

    A cikin wata takarda da ma'aikatar harkokin wajen ƙasar ta fitar, ta umarci ofisoshin jakadancinta a ƙasashen su daina bayar da bizar, yayin da ake ci gaba da yin bita kan matakan da ake bi wajen tantancewa.

    Dakatarwar za ta soma aiki ne nan da mako guda, kuma babu tabbacin tsawon lokacin da za a ɗauka kafin a janye ta.

  3. 'An kaddamar da shirin kawo ƙarshen yaƙin Gaza'

    Gaza

    Asalin hoton, Reuters

    Wakilin Trump na musamman a Gaza ya sanar da ƙaddamar da mataki na biyu na shirin kawo ƙarshen yaƙin Gaza.

    A wannan matakin, za a kafa gwamnatin ƙwararru a Gaza, sannan za a ƙwance ɗamarar ƙungiyar Hamas, kuma sojojin Israila za su janye.

    Zuwa yanzu dai Hamas ta ƙi amincewa ta miƙa makamanta, haka-zalika Isra'ila ta ƙi amincewa da ficewa baki ɗaya daga Gaza.

    Yarjejeniyar da aka cimma na tsawon watanni uku na da rauni.

    Ma'aikatar lafiya ta Gaza ta ce Falasɗinawa fiye da 400 suka mutu a hare-haren Isra'ila tun bayan tsagaita wuta.

  4. Yadda wasan Najeriya da Moroko ke wakana

    Najeriya da Moroko na can suna fafatawa a wasan dab da karshe na gasar cin kofin Afirka.

    Akwai shafi na musamman da ke kawo rahotanni kan wasan....

    Afcon

    Asalin hoton, Getty Images

  5. Gwamnati da ASUU sun cimma yarjejeniyar inganta tsarin ilimin jami'o'i

    ASUU

    Asalin hoton, Getty Images

    Gwamnatin Najeriya da ƙungiyar malaman jami’o’in ƙasar (ASUU) sun rattaɓa hannu kan sabon tsarin yarjejeniya domin inganta tsarin ilimin jami’o'in ƙasar.

    ASUU ta ce sabuwar yarjejeniyar da aka cimma, za ta taimaka wajen inganta harkokin koyo da koyar wa a jami’o’in ƙasar.

    Ƙungiyar ta ce yarjejeniyar za ta kuma kawo ƙarshen tafiya yajin aiki da ake yawan yi saboda gazawar ɓangaren gwamnati na mutunta yarjejniyar da suka cimma tun 2009.

    Shugaban ƙungiyar ta ASUU reshen jami’ar Bayero da ke Kano, Farfesa Ibrahim Tajo, ya ce abubuwan da sabuwar yarjejniyar ta ƙunsa sun haɗa da ƙarin albashi da kashi 40 da kuɗaɗen bunƙasa bincike da na gwaje-gwaje da kuma sauran harkokin koyarwa.

  6. Amurka ta fara kwashe dakarunta daga Qatar

    US

    Asalin hoton, TSGT Scott Reed, USAF

    Rundunar sojin Amurka na kwashe dakarunta da ke wasu sansanoninta a yankin Gulf, yayin da shugaba Trump ke duba yiwuwar bayar da umurnin kai wa Iran harin soji sakamakon zanga-zangar ƙin jinin gwamnati.

    Rahotanni sun bayyana cewa ana kuma janye ƙananan ma'aikatan Birtaniya daga sansanin Al Udeid na Qatar, wanda aka kai wa hari a yaƙin da Iran da Isra'ila suka yi na kwanaki 12 a shekarar da ta wuce.

    Jami'ai a Amurka sun ce kwashe dakarun wani mataki ne na kandagarki.

    Trump ya yi gargaɗin ɗaukar mummunan mataki idan Iran da rataye masu zanga-zanga.

  7. Senegal ta kai wasan karshe

    Afcon

    Asalin hoton, Getty Images

    Shikenan an tashi wasa!

    Kwallon Sadio Mane ta kai Senegal wasan karshe na gasar cin kofin Afirka.

    Burin Mohamed Salah na cin Afcon ya sake zuwa karshe.

    Senegal da ta lashe Afcon a 2021 za ta hadu da duk wadda ta yi nasara anjima tsakanin Najeriya da Moroko, a wasan karshe da za a yi ranar Lahadi.

  8. Masar na da sauran minti biyar domin samun damar farkewa.

  9. Gooaaaaal

    Sadio Mane ya ci wa Senegal kwallonta na farko a wannan fafatawa.

    Afcon

    Asalin hoton, Getty Images

  10. 'Tattalin arzikin Najeriya na kan hanyar bunƙasa'

    Kuɗi

    Asalin hoton, Getty Images

    Bankin Duniya ya ce tattalin arzikin Najeriya na kan hanyar bunƙasa mafi girman cikin fiye da shekara goma.

    Ana hasashen cewa zai ƙaru da kashi 4.4 cikin 100 a shekarun 2026 da 2027.

    Bankin ya bayyana hakan ne a sabon rahotonsa na ci gaban tattalin arzikin duniya wato Global Economic Prospects da ya fitar a ranar Talata.

    Sai dai masana na cewa hasashen ya yi hannun riga da halin rayuwa da al’ummar ƙasar ke ciki.

  11. Masar ba ta taɓuka wani abin kirki a gidan Senegal.

    Babu haɗin-kai tsakanin ƴan wasan baya da kuma na gaba.

  12. An koma zagaye na biyu

    An koma zagaye na biyu a wasan daf da karshe da ake fafatawa tsakanin Masar da Senegal.

  13. An fara bincike kan mutuwar tsohuwar minista a Burkina Faso

    Hukumomin shari’a a Burkina Faso sun bayyana cewa sun fara bincike kan mutuwar wata tsohuwar ministar gwamnati, bayan da aka tsinci gawarta a gidanta da ke birnin Ouagadougou.

    Masu gabatar da ƙara sun ce shaidu na farko sun nuna cewa an kai mata hari ne tare da kashe ta.

    An gano gawar Yolande ne ranar Asabar a gidanta da ke unguwar Karpala a birnin.

    Babban mai gabatar da ƙara, Lafiama Prosper Thombiano, ya ce an ɗauki lamarin a matsayin abin gaggawa, inda aka tura jami'an tsaro da ƙwararrun masana binciken gawarwaki domin gano yadda mutuwar ta faru da kuma gano waɗanda ke da hannu.

    Hukumomi sun kuma yi kira ga jama’a da su taimaka da bayanan da za su taimaki bincken.

    Marigayiyar ta kasance fitacciyar ’yar siyasa a lokacin mulkin tsohon shugaban ƙasar Blaise Compaoré, wanda ya mulki Burkina Faso na tsawon shekaru 27 kafin kifar da shi a juyin-juya-halin jama’a na shekarar 2014.

  14. An tafi hutun rabin lokaci

    Alkalin wasa Pierre Ghislain Atcho ya busa tafiya hutun rabin lokaci daf da lokacin da Senegal ke shirin bugun kusurwa.

    Babu ci tsakanin ƙungiyoyin zuwa yanzu.

  15. Mohamed Salah ya samu katin gargaɗi, bayan da ya riƙe tsohon ɗan wasan Liverpool Sadio Mane, bai ji daɗin katin ba.

    Ɓangarorin masu horar da tawagogin ƙasashen biyu duka sun harzuka a bayan fili.

  16. Pape Gueye ya yi ƙoƙarin buga kwallo a kusa da ragar Masar, sai dai bai buga kwallon da ƙarfi ba - ba ta yi haɗari ba.

    Senegal na da shot huɗu yayin da Masar ba ta da ko ɗaya kawo yanzu.

  17. Senegal na ci gaba da mamaye wasan, sai dai ƴan wasan Masar na ƙoƙari wajen ganin sun dawo sun tsare gida da hana abokan karawarsu samun dama mai kyau.

    Babu ƙungiyar da ta samu ƙwaƙƙwarar dama zuwa yanzu.

  18. 'Fitar Koulibaly babbar asara ce ga Senegal', Courtney Sweetman-Kirk, tsohuwar ƴar wasan Liverpool

    Koulibaly ba zai ji daɗin fita ba daga wannan wasa. Babbar asara ce a wajen ɗan wasan, musamman ma irin jagoranci da ke yi wa tawagar.

  19. Jim kaɗan bayan samun katin gargaɗi, kyaftin ɗin Senegal Kalidou Koulibaly ya ji ciwo sannan ya kwanta a ƙasa.

    Da alama raunin ba mai sauki bane.

    Za mu iya cewa watakila ya buga wasansa na karshe a wannan gasar.

    Afcon

    Asalin hoton, Reuters

  20. Ɗan wasan gaban Senegal Nicolas Jackson ya karɓi kwallo, inda ya ɗaɗa ta zuwa gidan Masar sai dai kwallon ta yi sama ta fita.

    Wannan wata dama ce da tsohon ɗan wasan na Chelsea ya samu - amma ba ta yi amfani ba yanzu.