Buhari: 'Ba na yin barci a bakin aiki'

Shugaba Buhari

Asalin hoton, Facebook/Nigeria Presidency

Lokacin karatu: Minti 1

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya mayar da martani ga Bishop na Yola Stephen Mamza wanda ya ce ci gaba da kashe-kashen da ake yi a kasar wata manuniya ce ga "yadda shugaban yake barci a bakin aikinsa."

Shugaban ya mayar da martanin ne ta bakin babban mai taimaka masa a fannin yada labarai Malam Garba Shehu a ranar Litinin.

A lokacin wa'azinsa na bikin Easter, Bishop Mamza, ya soki gwamnatin Buhari kan yadda ta kasa kawo karshen kashe-kashe da satar mutane don neman kudin fansa.

Garba Shehu ya wallafa a shafinsa na Facebook cewa Babban Limamin Katolika na Yola bai yi ya Shugaba Buhari adalci ba, inda ya ce "an samu ci gaba sosai a shekaru uku zuwa hudu da suka gabata a ciki da wajen garin Yola."

Ya ci gaba da cewa:"Wannan ci gaban da aka samu ba zai yiwu ba, idan da a ce shugaban bacci yake yi."

Kauce wa Facebook

Babu karin bayanai

Ci gaba da duba FacebookBBC ba za ta dauki alhakin abubuwan da wasu shafukan daban suka wallafa ba.

Karshen labarin da aka sa a Facebook

Ya ce "kimainin 'yan gudun hijira 400,000 da ke samun mafaka a Adamawa yanzu sun koma Borno - abin da ya sa aka samu dimbin fitowar masu kada kuri'a a yankin Arewa maso Gabas lokacin zabe."

Har ila yau ya ce: "Bayan garin Yola, garuruwan Michika da Madagali da Mubi wadanda a baya suke karkashin ikon Boko Haram, tuni suka dawo hannun dakarun sojin Najeriya."

A karshe Malam Garba Shehu ya ce "yankin Arewa maso Gabashin kasar ya samu ci gaba fiye da yadda yake a lokacin gwamnatin baya."