ASUU: Yaushe kungiyar malaman jami'a za ta daina yajin aiki?

Malaman jami'a

Tattaunawar da ake yi tsakanin gwamnatin tarayyar Najeriya da kungiyar malaman jami'a ta ci tura lamarin da ya jefa dubban daliban kasar cikin mawuyacin hali.

Hakan ya sa dalibai kamarsu Olamide Tejuoso wadda ke fatan soma shekarar 2019 za su ci gaba da zaman gida.

News image
Muhammadu Buhari
APC za ta aiwatar tare da tabbatar da tanadin da aka yi wa dokokin ilimin bai-daya musamman mayar da hankali kan daidaito wajen daukar dalibai a makarantun firamare da sakandare tare da inganta yanayin karatun da kuma makarantun. Muna fatan ware kashi 15 na kasafin kudi kan wannan fanni wanda ya kunshi horar da malamai a ko wane fanni na ilimi.
Tabbatar da gaskiya

Dokar karatun ba-daya da aka amince a 1999, ta ce dole gwamnati ta bayar da ilimin firamare na shekaru shida kyauta. Sannan dalibai za su shiga matakin farko na karatun sakandare ba tare da an biya kudi a jiha ba.

Babu inda aka ambaci daidaito wajen ilmantar da yara maza da mata, amma a Najeriya yara maza ne suka fi zuwa makaranta fiye da mata - Duk a cikin mata tara a makaranta akwai maza guda 10.

An fi ba da muhimmanci kan kara yawan dalibai mata a makarantu

Hukumar kula da ilimi ta Majalisar Dinkin Duniya Unesco ta kayyade daidaito tsakanin maza da mata inda ta ce idan aka samu maza 100 a makaranta ya kamata a ce an dauki mata 98 zuwa 102.

A cewar wani bincike kan ilimi a 2016, kasa da jiha daya cikin uku ake samun daidaiton jinsi a makarantun firamare. A matakin farko na sakandare kuma jihohi tara ne, jihohi uku kuma a matakin karshe na sakandare

Jihar Ekiti ce kan gaba wajen samun daidaito tsakanin maza da mata a duk matakin na ilimi a jihar.

Jihar Katsina ce ta karshe da aka fi samun rashin daidaito a dukkanin matakan ilimi bisa ga yawan dalibai a makarantu. An dauki sama da yara maza 170,000 fiye da mata a makarantun firamare; sama da maza 43,000 fiye mata a matakin farko na sakandare da kuma maza sama da 44,500 fiye da mata a matakin karshe na sakandare.

Jihar Zamfara ce mafi muni ta la'akari da yawan daliban da aka dauka a makarantu a dukkanin matakai na ilimi inda adadin maza ya lulluka na dalibai mata.

Ingancin ilimin da wadannan daliban ke samu shi ma wani batun diba wa ne. Sakamakon wani binciken ilimi na 2015 (NEDS), ya nuna cewa kashi 44 na daliban da ke makarantun firamare na gwamnati sun iya karatu, amma a makarantu masu zaman kansu kashi 74 ne suka iya karatu. A matakin sakandare kuma a makarantun gwamnati kashi 91 ne yayin da masu zaman kansu kashi 96.

Shugaba Buhari ya yi alkawalin ware wa ilimi kashi 15 a kasafin kudi, amma ayyukansa tun hawansa ya nuna akwai bukatar mayar da hankali sosai domin cimma wannan burin

A 2016, kashi takwas gwamnatinsa ta ware wa ilimi a kasafin kudi, a 2017 adadin ya ragu zuwa kashi 7.4. A 2018 kuma an sake ware wa ilimi kashi bakwai daga kasafin kudin wato Naira biliyan 650.

Domin cika alkawalin da ya dauka na ware wa ilimi kashi 15 a kasafin kudi, shugaban dole sai ya lunka kudaden da yake ware wa ilimi wato naira tiliyan 1.3, ko ya rage kudaden da aka ware wa wani bangare.

News image
Atiku Abubakar
Muna kashe naira tiliyan daya domin biyan albashin sojoji da jami'an tsaro, kasa da kudaden da muke biyan albashi a bangaren ilimi.
... 12 ga Agustan 2018 (Tattaunawa da jaridar ThisDay)
Tabbatar da gaskiya

A 2018, gwamnatin Tarayya ta ware wa ilimi naira biliyan 650, kusan kashi biyu bisa uku za a kashe su ne ga biyan albashi.

Amma kudaden da ake kashewa wajen biyan albashi a bangaren ya kusan yin daidai da kasafin kudin da aka ware wa ma'aikatar tsaro kuma kadan ne kawai ake kashe wa ga biyan albashi.

Duk a 2018, gwamnati ta shirya kashe naira biliyan 418 ga ma'aikatar tsaro wanda ya kusan yin daidai da adadin kudaden da ake biyan albashi a bangaren ilimi.

Idan aka diba kudaden da ake bian sojoji da sauran jami'ai, naira biliyan 12.2 aka ware domin biyan albashin sojoji.

Idan aka hade da adadin kudaden albashin sauran jami'an tsaro, (naira biliyan 164), jimillar kudin bai kai rabin kudaden da gwamnati ke kashewa ba ga biyan albashi a bangaren ilimi, kuma ko kadan bai yi kusa da naira tiliyan daya ba Atiku ke ikirari.

Ko wannan albashin ya kai ko bai kai ga wadanda ke da hakki ba wani batu ne na daban.

Wasu alkalumman bincike game da albashi da wata kungiya da ke sa ido kan yadda ake kashe kudi wato BudgIT ta fitar a 2018, ta ce akalla 12 daga cikin jihohi 35 sun ce sun kasa biyan malaman makarantu albashin da suke bin su.

Karin bayaniLatsa nan don karin bayani

    News image
    Tabbatar da gaskiya

    Ta so kammala karatun digirinta domin ta soma aiki da wani kamfani a matsayin mai samun horon aiki. Matakin farko da take son dauka domin zama marubuciya bayan ta kammala digiri a jami'ar Ibadan.

    Sai dai maimakon hakan, wannan daliba da take karatu a fannin aikin jarida, ta fada cikin matukar damuwa saboda yajin aikin da malaman jami'a ke yi.

    Malaman sun zargi gwamnati da kin yin biyayya ga yarjeniyoyin da suka kulla a baya game da inganta tsarin karatun gaba da sakandare.

    Sun daka yajin aikin ne saboda ba a bai wa makarantun kudaden da suka kamata da kuma rashin gine-gine da ma yunkurin kara kudin makaranta.

    Ranar Litinin kungiyar malaman jami'a da ministan kwadagon Najeriya Chris Ngige sun yi taro inda suka ce sun cimma matsaya. Gwamnati na shirin bai wa jami'o'in 15.4bn naira.