An sace wani baturen Jamus a Nijar

Gwamnatin Jamhuriyar Nijar ta ce an sace wani Bajamushe da ke gudanar da ayukan jin-kai a kusa da iyakar Mali.

A cewar ministan shari'a kuma Antoni-Janar din kasar, 'yan bindiga a kan babura ne suka sace mutumin mai suna, Joerg Lange, a garin Inates da ke yammacin kasar.

Kawo yanzu dai babu wani cikakken bayani a kan 'yan bindigar.

Sai dai mayakan jihadi da ke da alaka da al-Qaeda da Kungiyar IS, sun sha kai hare-hare a kan jami'an tsaro da fararen hula a iyakar kasar da Mali.