Tunisia: Ana zanga-zangar kan tashin farashin magani

Riot police on the streets of Tunis, Tunisia. Photo: 10 January 2018

Asalin hoton, Reuters

Bayanan hoto, 'Yan sanda sun yi amfani da hayaki mai sa hawaye domin tarwatsa dimbin mutane da ke zanga-zanga kan tsadar kayayyakin masarufi.

An kama mutane fiye da 300 a kasar Tunisiya ranar Laraba daddare, game da zanga-zangar kin jinin gwamnati da yan kasar suke yi.

'Yan sanda sun sa wa mutanen da zanga-zanga kan tashin frashin kayayyakin masarufi hayaki mai sa hawaye.

An kai sojoji garurruwa daban-daban a kasar domin kare gine ginen gwamnati inda masu zanga-zangan suke.

Firayim ministan kasar, Youssef Chahed, ya nuna bacin rai game da lalata kayan gwamnati da masu zanga-zangar suke yi, yana mai cewa suna kokarin karya gwamnati ne.

Mene ne makasudin zanga-zanzar?

An gudanar da zanga-zangar a akalla wurare 10 a fadin kasar ciki har da birnin Tunis.

A makon da ya gabata ne aka fara zanga-zangar cikin lumana, amma a ranar litinin da yamma zanga-zangar ta zama ta tashin hankali, inda aka kama mutane kusan 600 tunda aka fara tashin hankalin a makon ya gabata.

Mai magana da yawun ma'aikatar cikin gida, Khelifa Chiban, ya fada wa kafafan watsa labarai cewa an kama mutane fiye da 300 a ranar Laraba kawai.

A demonstrating graduate shouts slogans during protests against rising prices and tax increases, in Tunis, Tunisia January 9, 2018

Asalin hoton, Reuters

Bayanan hoto, Mutane suna neman a kawo karshen matakan tsuke bakin aljihu

Daya daga cikin masu zanga-zangar ya fada wa BBC cewa suna yin zanga-zangar ne dan tsadar rayuwa a kasar.

''Kudin magani ya karu, har da komai ma, amma ba'a kara albashi ba. Ba na jin yanzu ne lokacin da komai zai yi tsada."

Ana shirin yin wata gagarumar zanga-zangar a ranar jumma'a.

Masu zanga zangar suna bukatar gwamnatin ta soke kasafin kudin 2018, wanda kungiyoyin 'yan adawa suka ce yana cike da rashin adalci.