Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.
Alhazan Nigeria bakwai sun mutu a Saudiyya
Wasu alhazan Najeriya bakwai sun mutu a Saudiyya gabanin a fara aikin Hajji.
Alhazan sun fito ne daga jihohin Kwara, da Katsina da Kogi da kuma Kaduna.
Sannan wata Hajiya daga Jihar Kogi ta Haihu a Madina. Shugaban NAHCON Abdullahi Mukhtar, ya ce za a hukunta jihar da matar ta fito ta hanyar rage mata kujeru a badi, da kuma hukunta shugabannin hukumar aikin hajji ta jihar.
Alhazan Nigeria Kusan dabu 90 ne ke halartar aikin hajjin bana.