Alhazan Nigeria bakwai sun mutu a Saudiyya

Wasu alhazan Najeriya bakwai sun mutu a Saudiyya gabanin a fara aikin Hajji.

Alhazan sun fito ne daga jihohin Kwara, da Katsina da Kogi da kuma Kaduna.

Sannan wata Hajiya daga Jihar Kogi ta Haihu a Madina. Shugaban NAHCON Abdullahi Mukhtar, ya ce za a hukunta jihar da matar ta fito ta hanyar rage mata kujeru a badi, da kuma hukunta shugabannin hukumar aikin hajji ta jihar.

Alhazan Nigeria Kusan dabu 90 ne ke halartar aikin hajjin bana.