Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.
Sanwo-Olu zai yi tazarce a Lagos
An bayyana gwamnan jihar Legas Babajide Sanwo-Olu a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamnan jihar a karo na biyu.
Babban jami'in tattara sakamakon zaɓe na jihar Professor Adenike Temidayo Oladiji ya ce Sanwo-Olu ya yi nasara da ƙuri'u 762,134.
Jam'iyyar LP ce ta zo ta biyu inda ɗan takararta Gbadébo Rhode-Vivour ya samu ƙuri'u 312,329, sai kuma ɗan takarar jam'iyyar PDP Abdulazeez Olajide Adeniran da ya zo na uku da ƙuri'u 62,449.
A zaɓen shugaban ƙasa da aka yi a watan Fabrairu, jam'iyyar LP ce ta samu gagarumar nasara a jihar Lagos, wacce ita ce mahaifar ɗan takarar shugaban kasa na jam'iyyar APC, kuma a yanzu shugaba mai jiran gado.