'An yi kuskuren ba da kyautar Nobel' - 'Yan Eritrea

'Yan kasar Eritrea a Scandinavia na gudanar da zanga-znagar adawa da kyautar Nobel kan samar zaman lafiya da ake shirin bayarwa ga firai minista Abiy Ahmad.

A yau ne aka mika wa Abiy Ahmed kyautar, bayan Kwamitin Nobel ya zabi firaminista shi a matsayin wanda ya ci kyautar ta bana, saboda kawo karshen rikici da tsattsamar dangantaka tsakanin kasarsa da makwabciyarta Ethiopia da aka shafe fiye da shekaru ashirin ana yi.

Masu zanga-zangar a Oslo sun ce alfanon sasanci tsakanin Eritrea da Ethiopia basu tabbata ba, don haka firami minista Abiy bai cancanci kyautar ta Nobel ba.

Daruruwan mutane ne ke zanga-zangar da suka gana da wani dan majalisar dokokin kasar Norway a birnin Oslo, na dauke da kwalaye dake cewa: "Kyautar Nobel ta tabbatacciyar zaman lafiya ne, ba siyasa ba."

Wani daga cikin masu zanga-zangar ya sheda wa BBC cewa tun da aka rattaba hannu a kan yanrjejeniyar zaman lafiyar a bara, babu wani sauyin da aka samu a fagen siyasar Eritrea.

Ya kara da cewa har yanzu ba a sanya alamomi ba a iyakokin kasashen da aka rufe.

Kungiyoyin kare hakkin bil'adama na yawan sukan gwamnatin Eritrea wadda ba zaben ta aka yi ba.