Kocin Liverpool, Jurgen Klopp ya ce zai kare kofin Premier a badi

Liverpool boss Jurgen Klopp

Asalin hoton, PA Media

Bayanan hoto, Liverpool won the Champions League under Klopp last season

Kocin Liverpool, Jurgen Klopp ya ce za su ci gaba da salon kai hare-hare a wasannin kakar badi, maimakon tsare gida.

A makon jiya Liverpool ta lashe kofin Premier League na bana, kuma na farko tun bayan shekara 30, kuma saura wasa bakwai-bakwai a kammala wasannin bana.

Klopp wanda ya koma Liverpool a 2015 ya ce ''Za mu kare kofin da muka lashe za kuma mu ci gaba da salon kai hare-hare.

Liverpool ta bai wa Manchester City tazarar maki 23, wacce za ta fafata da ita ranar Alhamis a gasar Premier League.

Klopp ya ce ''A kakar badi Manchester United da Chelsea za su kara karfin kungiyoyinsu.''

''City za ta ci gaba da taka rawa a badi, United da Chelsea suna kan ganiya, musamman kungiyar Stamford Bridge na saka kwazo.''

Chelsea ce ta doke Manchester City 2-1 a Stamford Bridge da ya bai wa Liverpool damar lashe Premier League na bana saura wasa bakawi-bakawi a karkare kakar bana.