Da gaske EFCC na farautar 'ya'yan Atiku?

Asalin hoton, Getty Images
Hukumar EFCC ta musanta zargin da PDP ta yi cewa ta kai samame a gidan 'ya'yan dan takararta na shugaban kasa Alhaji Atiku Abubakar.
A wasu jerin sakwanni da ta wallafa a Twitter, EFCC ta ce ta kai farmaki ne a gidan 'ya'yan tsohon gwamnan jihar Abia Theodore Orji a Maitama wanda take gudanar da bincike a kansa.
Kuma 'ya'yan tsohon gwamnan na Abia suna makwabtaka ne da Aliyu da Mustapha Atiku Abubakar tsohon mataimakin shugaban kasa kuma dan takarar jam'iyyar PDP a zaben 2019.
Sai dai kuma Jam'iyyar PDP ta yi zargi cewa, EFCC ta kai samamen ne a gidan 'ya'yan na Atiku bisa umurnin fadar shugaban kasa.
Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.
Karshen labarin da aka sa a X, 1
Fadar shugaban kasa ta musanta zargin, inda mai magana da yawun shugaban kasa Malam Garba Shehu ya soki PDP da yada labaran karya.
Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.
Karshen labarin da aka sa a X, 2
"A Najeriya yanzu babu wanda ya fi yada labaran karya kamar jam'iyyar PDP," in ji Garba shehu a sakon da ya wallafa a Twitter.
EFCC ta ce binciken da take yi kan tsohon gwamnan Abia Theodore Orji, kan halatta kudaden haramun ne ya shafi 'ya'yansa.
Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.
Karshen labarin da aka sa a X, 3
Hukumar ta ce ta kai ga kama 'ya'yan tsohon gwamnan ne ta hanyar bin sawun wasu manyan motocin da aka ce nasu ne.
Kuma a lokacin da take tatsar bayanai ne suka bayyana mata gidan da suke zama a Abuja da ta kai samame a ranar Asabar.
EFCC ta ce bincikenta da ta gudanar bai shafi bangaren gidan 'ya'yan Atiku ba.
Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.
Karshen labarin da aka sa a X, 4
Sai dai a cikin bayanan da ta wallafa a Twitter, hukumar ba ta ce ko ta leka sashen gidan 'ya'yan Atiku ba da suke gida guda da 'ya'yan tsohon gwamnan na Abia da ta kama.











