Iran ta naɗa Alireza Arafi jagoran addinin ƙasar na riƙo

Asalin hoton, intanet
Hukumomin Iran sun sanar da naɗin, Ayatollah Alireza Arafi matsayin jagoran addinin ƙasar na riƙo, kafin a zaɓi sabo.
Majalisar manyan malaman ƙasar mai mambobi 88 ce za ta za bi sabon jagoran addinin.
Al'ummar kasar ne dai ke zabar mambobin majalisar bayan kowace shekara takwas.
A ƙarƙashoin dokokin Iran, waɗannan manyan malaman ne ke da alhakin zaɓen sabon jagoran addini da zarar wanda yake kan muƙamin ya kau, to sai dai ana ganin hakan zai yi wahala kasancewar babu kwanciyar hankali a ƙasar da ke cikin yanayi na yaƙi.









