An kashe mutane fiye da 30 a Borno

Rahotanni daga garuruwa hudu na jihar Borno sun ce mutane fiye da talatin sun mutu a hare-hare da ake zarin 'yan Boko Haram sun kai.
Haka kuma bayanai sun nuna cewar an kona gidaje tare da jikkata wasu mutane da dama.
Lamarin ya auku ne a garuruwan Krenuwa da Moforo da Kimba da kuma Kubribu.
Harin na zuwa ne a daidai lokacin da 'yan Boko Haram ke tsananta hare-hare a wasu kauyukan jihar Borno.
Sannan kuma ga 'yan mata dalibai fiye da 200 da aka sace a Chibok da ke jihar Borno.
Kungiyar Boko Haram ta kashe dubban mutane musamman a jihohin Borno da Yobe da kuma Abuja babban birnin kasar.







