Bayanai kan ƴan takarar gwamnan jihar Ekiti na 2022

Ekiti

Asalin hoton, Others

A ranar Asabar 18 ga watan Yuni ne za a yi zaɓen gwamnan jihar Ekiti na 2022.

Duk wanda ya yi nasara a zaɓen zai maye gurbin gwamna mai barin gado Kayode Fayemi na jam'iyyar APC, wanda a cikin shekarar nan wa'adin mulkinsa zai ƙare.

Tun a watan Janairu ne jam'iyyu suka gudanar da zaɓukan fitar da gwanayensu, kuma sunayen waɗanda hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasar INEC ta tantance ne kawai za su kasance a kan ƙuri'ar zaɓen.

Ga dai bayanan wasu ƴan takarar da INEC ɗin ta tantance. An zaɓe su ne bisa waɗanda BBC ta iya samun su ko bayanansu a intanet, ba don wani ya fi wani ba.

Ƴan takarar gwamna na Ekiti

  • Sana'a: Ma'aikacin gwamnati
  • Shekaru: 55
  • Biodun Abayomi ɗan asalin Ikogosi-Ekiti ne a jihar Ekiti
  • Ya taɓa zama mai bai wa gwamnan Ekiti shawara na musamman a kan harkokin majalisa daga 8 ga watan Yunin 1999 zuwa 2000 da kuma daga 1 ga Agusta zuwa Satumban 2001.
  • Ya taba riƙe muƙamin shugaban ma'aikata na fadar gwamnatin jihar Ekiti daga Satumban 2001 zuwa 29 ga watan Mayun 2003.
  • Oyebanji ya taɓa rike muƙamin Kwamishinan Kasafin Kuɗi da Tsare-tsare na jihar Ekiti, daga 10 ga Janairun 2013 zuwa 16 ga Oktoban 2014, sannan kuma ya riƙe muƙamin Sakataren gwamnatin jihar daga 16 ga Oktoban 2018 har zuwa 7 ga Disamban 2021.
  • Sana'a: Ma'aikacin gwamnati
  • Shekaru: 64
  • Kolawole ya taɓa zama shugaban jam'iyyar PDP a jihar Ekiti kafin ya yi murabus a watan Satumban 2021 don tsayawa takarar gwamna.
  • A lokacin mulkin tsohon gwamnan jihar, Ayo Fayose, ya riƙe muƙamin kwamishinan muhalli daga tsakanin 2015 zuwa 2018.
  • Ya wakilci mazaɓar Efon a majalisar dokokin jihar daga tsakanin shekarar 2007 da 2011.
  • Shi ɗan asalin garin Efon Alaaye ne a jihar Ekiti.
  • Sana'a: Tsohon gwamnan Ekiti
  • Shekaru: 67
  • Olusegun Oni tsohon gwamnan Ekiti ne daga tsakanin 29 ga watan Mayun 2007 zuwa 14 ga Oktoban 2010.
  • Oni na daga cikin waɗanda suka ƙirƙiri jam'iyyar UNCP a siyasar jihar Ekiti, inda ya taka rawa a matsayin jigo kuma ɗan gani kashenin jam'iyyar.
  • A shekarar 2014 ne ya koma APC daga PDP. A 2019, jam'iyyar APC a mazaɓar Ifaki-Ekiti a ƙaramar hukumar Ido/Osi ta dakatar da shi kan zargin yi wa jam'iyya zagon ƙasa, daga baya ya sake barin APC zuwa PDP. A watan Fabrairun 2022 ne ya bar PDP zuwa SDP bayan da ya sha kaye a zaɓukan fitar da gwani.
  • Sana'a: Ma'aikacin gwamnati
  • Shekaru: 62
  • Adebowale Ranti Ajayi ɗan asalin Emure Ekiti ne a yankin kudancin jihar.
  • Shi ne kwamishina na farko na kasafi da tsare-tsaren tattalin arziki a jihar, amma kafin nan ya riƙe muƙamin kwamishinan Kasuwanci da Zuba jari da ƙirƙire-ƙirƙire a gwamnatin Dr Kayode Fayemi.
  • Mamba ne na jam'iyyar APC kafin ya koma jam'iyyar YPP har ma ya tsaya takara a ƙarƙashinta.