Afenifere ta gargadi ƙungiyar dattawan Arewa kan kare makiyaya

Afenifere

Asalin hoton, Google

Ƙungiyar Yarbawa ta Afenifere ta ja kunnen ƙungiyar tuntuɓa ta Arewacin Najeriya game da yin duk wasu kalamai da ka iya zama goyon baya ga makiyaya da aka bai wa wa'adin ficewa daga wasu jihohin kudu maso yammacin ƙasar.

Ita dai ƙungiyar tuntuɓa ta arewacin Najeriya ta yi gargaɗin cewa kokarin korar makiyaya daga wani yanki na kasar da kuma harin da aka kai musu kwanan nan a jihar Oyo, na iya kawo barazana ga zaman lafiyar Najeriya.

Sai dai cikin wata sanarwa da Afenifere ta Yarbawa ta fitar, ta ce dole ne al'ummarsu ta kare kanta daga abin da ta kira "wasu da suka fi fifita shanunsu fiye da dan adam".

Afenifere ta ce masu barazana da yakin basasa su kwana da sanin cewa al'ummarta ba kanwar lasa ba ce, don haka ba za ta naɗe ƙafa tana kallo a ci gaba da kisan jama'ar yankin ba.

Sai dai masana a fannin tsaro kamar su Barista Audu Bulama Bukarti na kira ga gwamnatin tarraya da ta ɗauki matakan da suka dace kan lamarin tsaro a fadin ƙasar baki daya.

Ramuwar gayya

Disputes over grazing rights have led to tensions between herdsmen and farmers

Asalin hoton, Getty Images

Kwararren lauyan ya ce tun farko lamarin ya faro ne sakamakon gazawar gwamnati wajen kare rayuka da dukiyoyin jama'a, lamarin da ya sa wasu ke ganin lokaci ya yi da ya kamata su tashi su kare kansu.

"Idan suka ci gaba da kai hari kamar yadda muka fara gani a yanzu, wannan zai sa ƴan uwan waɗanda ake kai wa hari a sauran sassan Najeriya su fara daukar matakin ramuwar gayya, daga nan kuma lamari ya lalace," in ji lauyan.

Gwamnan jihar Ondo Rotimi Akeredulu ne ya fara bai wa makiyaya a jiharsa wa'adin mako guda domin su fice daga cikin dazukan jihar, lamarin da ya janyo martani daga gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari.

A wani saƙo da mai taimaka wa shugaban ƙasar kan kafofin watsa labarai Malam Garba Shehu ya aika wa manema labarai, ya bayyana cewa fadar shugaban ƙasar na sane da wa'adin da aka bai wa makiyayan sannan tana bibiyar abubuwan da ke faruwa musamman kan batun matakin da gwamnan na Ondo ya ɗauka.

A cewarsa, rashin daidaito a irin yadda ake aika saƙo ne yake jawo ce-ce-ku-ce game da ainihin saƙon da ake so a aika wa jama'a.

"Babu wani abin cewa illa kira ga ɓangarorin su yi sulhu da kuma neman gwamnatin jihar da kuma shugabancin Fulani su ci gaba da tattaunawa domin fahimtar juna domin kawo ƙarshen rashin tsaron da ake fama da shi a jihar cikin sauri," in ji shi.