Dan Atiku Abubakar 'ya kamu da coronavirus'

Asalin hoton, Getty Images
Tsohon mataimakin shugaban kasar Najeriya, Atiku Abubakar ya ce dansa ya kamu da coronavirus.
Atiku Abubakar, ya bayyana hakan ne a wani sako da ya wallafa a shafinsa na twiiter.
Tsohon mataimakin shugaban kasar ya ce tuni aka kai dan nasa asibitin koyarwa da ke Gwagwalada a Abuja babban birnin tarayyar Najeriya inda ake masa magani.
Atiku Abubakar ya bukaci al'umma da su saka dan na sa a addu'a.

Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.
Karshen labarin da aka sa a X
Ya zuwa yanzu dai a hukumance akwai mutum 30 da suka kamu da cutar coronavirus a Najeriya, inda ake kyautata zaton cewa dan Atiku ne cikamakin mutum na 30 a jerin wadanda suka kamu da cutar a kasar.
Hukumar takaita yaduwar cutuka ta kasar dai ba ta sanar da suna ko wurin da wadanda suka kamu da cutar suke.
Mutanen da ke dauke da annobar coronavirus a nahiyar Afirka sun zarce mutum 1,000 a karshen wannan makon kamar yadda hukumar da ke yaki da cututtuka ta nahiyar ta bayyana.
Kasar Uganda ta bayyana mutum na farko da ya kamu da cutar a kasar inda kasar ta ce wani fasinja ne da ya zo daga Dubai.










