Tsohon Shugaban Masar Hosni Mubarak ya rasu

Hosni Mubarak

Asalin hoton, Reuters

Tsohon shugaban kasar Masar Hosni Mubarak ya rasu yana da shekara 91.

Mubarak, wanda aka tumbuke daga kan mulki a 2011, ya rasu a wani asibiti da ke birnin Alkahira.

Mubarak ya shafe shekara 30 a kan mulki kafin juyin juya halin kasar Masar.

An same shi da laifi a kisan masu zanga-zanga yayin juiyin juya halin. A watan Maris din 2017 ne aka sauya hukuncin tare da sakin sa.

A ranar Talata ne gidan talbijin na kasar ya sanar da mutuwarsa. Amma tun kafin sannan da safiyar Talatar kafar yada labaran intanet ta Al-Watan ta sanar da mutuwar tasa a wani asibitin sojoji.

A karshen watan Janairu ne aka yi wa Mubarak tiyata. A ranar Asabar din da ta gabata ne dansa Alaa ya ce yana bangaren kula ta musamman a asibitin.

Mubarak wanda aka haifa a shekarar 1928, ya shiga rundunar sojin sama yana matashi kuma ya taka muhimmiyar rawa a yakin da aka yi tsakanin Ira'ila da kasashen Larabawa a shekarar 1973.

Ya zama shugaban kasa shekara biyar bayan nan, sakamakon kashe Shugaba Anwar Sadat da aka yi.

Ya taka muhimmiyar rawa a sasantawar zaman lafiya tsakanin Isra'ila da Falasdinu.

Amma duk da irin biliyoyin dalolin da Amurka ta samu na taimako a lokacin mulkinsa, rashin aikin yi da talauci da cin hanci sun ci gaba da samun wajen zama a kasar.

An fara samun tashe-tashen hankula a watan Janairun 2011, bayan da kasar ta bi sahun Tunusiya wajen yin zanga-zangar da ta hambarar da shugaban kasarsu.

Bayan an shafe kwana 18 ana rikici a Masar, sai aka tursasawa Hosni Mubarak suka daga mulki.