Majalisar dokokin Kano ta gabatar da ƙudurin tsige mataimakin gwamnan jihar

Asalin hoton, FB/Aminu Abdulsalam
Majalisar dokokin jihar Kano ta fara shirin tsige mataimakin gwamnan jihar, Aminu Abdulsalam, bisa wasu zarge-zarge da aka gabatar a kansa a gaban majalisar, ranar Alhamis.
Shugaban masu rinjaye na majalisar Lawal Hussaini ne ya gabatar da ƙudurin tsige mataimakin gwamnan kan zarge-zarge da suka haɗa da almundahana da kuɗin gwamnati a lokacin da ya shugabanci wasu hukumomin gwamnati.
A kan haka ne majalisar ta ce, kamar yadda doka ta tanada, ta yanke shawarar sanar da mataimakin gwamnan game da matakin da ta fara ɗauka na tsige shi.
A watan Janairu ne gwamnan jihar Kano Abba Kabir ya sanar da sauya sheƙa zuwa jam'iyyar APC mai mulki a matakin tarayya, daga jam'iyyar NNPP, wadda ya lashe zaɓe ƙarƙashin ta a shekarar 2023.
Sai dai mataimakin nasa Aminu Abdulsalam bai bi shi zuwa jam'iyyar ta APC ba.
Wannan ya haifar da muhawara, inda wasu daga cikin manyan masu riƙe da muƙaman siyasa a jihar suka fara neman mataimakin gwamnan ya sauka daga muƙamin nasa.
Muna sabunta wannan labari...







