Kashi 87 cikin 100 na matalautan Najeriya a Arewa suke - Bankin Duniya

Mabarata

Asalin hoton, Getty Images

Wani rahoto da Babban Bankin Duniya ya fitar ya nuna cewa kashi 87 cikin 100 na matalautan da ke Najeriya suna zaune ne a arewacin kasar.

Rahoton ya ce talauci a yankin kudu maso kudancin kasar ya yi gagarumar raguwa tsakanin 2011 da 2016.

A ranar Litinin ne Bankin Duniyar ya fitar da rahoton.

"Talaucin da ake fama da shi a arewacin kasar musamman a arewa maso yammaci yana ci gaba da karuwa.

''Kusan rabin matalautan mutane suna zaune ne a arewa maso yamma kuma kashi 87 na matalautan kasar na zaune ne a arewacin kasar," a cewar rahoton.

Rahoton ya kara da cewa: "Talaucin da ake fama da shi a kudancin kasar bai wuce kashi 12 cikin 100 ba inda ake samun bambanci tsakanin yankunan da ke kudancin kasar.

''An samu raguwar talauci a yankin tsakanin 2011-2016."

A yanzu dai kason yawan mataulatan da ke Najeriya ya zarce na Indiya, kamar yadda rahoton ya zayyana.