Shugaba Buhari ya tafi Birtaniya don halartar taron zuba jari

Nigeria President Muhammadu Buhari

Asalin hoton, PIUS UTOMI EKPEI

Lokacin karatu: Minti 1

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya tafi birnin Landan a ranar Juma'a domin halartar taron zuba jari na Birtaniya da Afirka.

Mataimaki ga shugaba Buhari kan yada labarai, Buhari Sallau ya wallafa a shafinsa na Facebook cewa tuni shugaban ya tashi daga filin jirgin sama na Nnamdi Azikwe International da ke Abuja.

Tun da farko dai fadar shugaban Najeriyar ce ta sanar da tafiyar shugaban a shafinta na Twitter a ranar Alhamis.

Kauce wa X
Ya kamata a bar bayanan X?

Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

Gargadi: Ana iya samun talla wanda ba na BBC ba ne

Karshen labarin da aka sa a X

Taron wanda za a yi ranar 20 ga watan Janairun nan, ya zama tafiyar Buhari ta farko zuwa wani wuri a shekarar 2020.

Firai Minsitan Birtaniya Boris Johnson ne zai zama mai massaukin baki na taron, wanda ake sa ran zai hado kan shugabannin kasashen Afirka da manyan 'yan kasuwa na duniya.

Ana fatan taron zai samar da sabbin damarmakin kasuwanci da zuba jari da samar da ayyuka, wanda zai amfani nahiyar Afirka da Birtaniya.

Shugaba Muhammadu Buhari tare da gwamnan jihar Abia

Asalin hoton, Buhari Sallau