Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.
Ko Najeriya ta rabu da cutar Polio?
Najeriya ta cika shekara uku ranar Laraba nan ba tare da samun wani mai dauke da kwayar cutar polio ba.
Wannan ranar dai tana da muhimmancin gaske kasancewar a tsarin hukumar lafiya ta duniya (WHO), dole sai kasa ta shafe shekara uku ba tare da kamuwa da cutar ba kafin a iya ayyana ta a matsayin wacce ba kwayar polio a cikinta.
Amma har yanzu ba a tabbata cewa babu polio a Najeriya ba.
Dole sai WHO ta gudanar da bincike domin tabbatar da lamarin kafin su iya bayyana cewa ba a samu bullar cutar a cikin shekaru uku ba a kasar.
Ba a sa ran cewa hakan zai faru kafin farkon shekara mai zuwa, a cewar shugaban kwamitin polio a Najeriya, DoktaTunji Funsho.
A shekarar 2012, Najeriya na da a kalla mutum 223 da suka kamu da polio wato rabin adadin wadanda ke da polio duk duniya kenan a cewar WHO.
Dokta Funsho ya alakanta wannan nasarar da raguwar rikice-rikice da ake yi da mayakan kungiyar Boko Haram.
Rikicin da ake yi da kungiyar Boko Haram a arewa maso gabashin Najeriya ne ya sa magunguna ba sa isa wasu yankunan jihar Borno.
Borno dai ita ce jiha wacce aka fi samun mutanen da suka kamu da Polio. A ranar 21 ga watan Augustar shekarar 2016 ne aka samu mutum na karshe wanda ya kamu da polio.