Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Asabar 17/01/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Asabar 17/01/2026

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Abdullahi Bello Diginza

  1. Ma'aikatar shari'a ta Amurka tana binciken ƴan jam'iyyar Democrat a Minnesota

    Ana binciken wasu fitattun ƴan jam’iyyar Democrat biyu a jihar Minnesota, kan zargin yunƙurin daƙile ayyukan jami'an shige da fice na tarayya (ICE), yayin da rikici ke ƙara ƙazancewa tsakanin gwamnatin Trump da shugabannin jihar.

    Gwamna Tim Walz da magajin garin Minneapolis Jacob Frey na fuskantar binciken ma'aikatar shari'a ta Amurka game da kalaman da aka yi kan jami'an hukumar shige da fice ta ƙasa (ICE), a cewar abokiyar hulɗar BBC a Amurka CBS News.

    Binciken ya zo ne a daidai lokacin da wani alƙali na tarayya ya takaita dabarun da jami'an ICE da sauran jami’an tsaro za su iya amfani da su a Minneapolis, tare da hana amfani da hayaƙi mai sanya hawaye da kuma kame masu zanga-zangar lumana.

    Zanga-zangar ta ɓarke a birnin bayan da wani jami'in hukumar ICE ya harbe wata mata Renee Good, mai shekaru 37 har lahira a makon da ya gabata.

    Sabbin bayanai kuma sun fito fili a ranar Juma'a game da mutuwar Good.

    Jami’an agajin gaggawa sun gano aƙalla raunukan harbin bindiga guda uku a jikin matar da kuma yiwuwar na hudu a kanta, kamar yadda rahotannin da gidan talabijin na CBS ya gani suka nuna.

  2. Harin jirgi mara matuƙi ya kashe mutum 36 a Habasha

    Aƙalla mutane 36 ne suka mutu yayin da 16 suka jikkata a wani harin da jirgin yaƙi mara matuƙi da aka kai kan dakarun sa-kai da ke taimakawa gwamnati a yankin Amhara na ƙasar Habasha, kamar yadda hukumomin yankin da mazauna yankin suka shaida wa BBC.

    An kai harin ne a ranar Alhamis, 15 ga watan Janairu, 2025, a wani sansanin ƴmayaƙan da ke gundumar Sehala Seyemt na yankin Waghimira.

    Jami’an gundumar sun ce an kai harin ne a lokacin da mayaƙan su ke wani taron bita a gaban sansanin.

    Shaidu sun ba da rahoton cewa an kuma lalata makaman da aka ajiye a wurin, kuma an kona sansanin baki ɗaya.

    A cewar mazauna yankin, an ajiye mayakan ne a sansanin domin hana dakarun Fano-da suka shafe fiye da shekaru biyu suna fafatawa da sojojin gwamnatin tarayya tun daga watan Afrilun 2023- daga shiga gundumar.

    A ranar da aka kai harin dai rahotanni sun ce mayaƙan na Fano na shirin kai wa mayaƙan na yankin hari, lamarin da ya sa jami’an gundumar suka bukaci jami’an tsaron tarayya su shiga tsakani.

    Ma’aikatan lafiya sun tabbatar da cewa an kai gawarwaki 10 da wasu mutane tara da suka jikkata zuwa wata cibiyar kiwon lafiya da ke kusa, yayin da karin mutum daya kuma ya mutu bayan isar su.

  3. Ƙasashen Turai sun soki barazanar Trump na sanya musu haraji saboda Greenland

    Shugaba Macron na Faransa ya kira barazanar harajin da Mista Trump ya yi a matsayin 'abin da ba za a amince da shi ba'.

    Ya yi nuni da cewa, ba za a rinjayi ƙasashen Turai da ƙarfi ba, kuma idan aka aiwatar da harajin, za su mayar da martani cikin haɗin kai.

    Hakazalika Firaministan Sweden (Ulf Kristersson) ya ce ba za a tursasa musu ba.

    Jamus ta ce ta yi la'akari da kalaman Mista Trump kuma tana tuntubar takwarorinta na Turai.

    Ƴan jam'iyyar adawa da dama a Biritaniya ma sun soki sanarwar ta Mista Trump.

    Kemi Badenoch, wadda ke jagorantar jam'iyyar Conservative ta ce ta amince da matsayar Firaminista Keir Starmer, cewa al'ummarta ce kawai za ta yanke shawara kan makomar Greenland.

  4. Trump zai sanya haraji kan ƙasashen Turai saboda taƙaddamar Greenland

    Shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da wani sabon tsarin harajin kan kasashen da dama da ke ke fitar da kayayyaki zuwa Amurka, daga ranar 1 ga watan Fabrairu.

    Trump ya ce waɗannan za su ci gaba da kasancewa har sai "lokacin da aka cimma yarjejeniya don sayarwa Amurka Greenland baki ɗaya''.

    A saƙon da ya wallafa a shafukan sada zumunta, Trump ya ce ƙasashe da suka haɗa da Denmark da Norway da Sweden da Faransa da Jamus da Burtaniya da Netherlands, da kuma Finland za a "ƙara masu harajin kashi 10 cikin 100 kan kayayyakin da ake shigarwa Amurka.

    A ranar 1 ga watan Yuni, za a ƙara wannan zuwa kashi 25 cikin 100, ya wallafa a kan shafinsa na Truth Social.

    Sanarwar da Trump ya yi game da harajin da zai ɗorawa ƙasashen da ke cikin ƙawancen ƙungiyar tsaro ta NATO na nuni da ci gaba a yunkurinsa na neman mallakar Greenland, duk da adawar gwamnatocin Turai.

    A cikin ƴan makonnin nan Fadar White House ta sha bayyanawa ƙarara cewa za a iya amfani da duk wani mataki yayinda shugaba Trump yake neman karɓe iko da tsibirin.

  5. Jagoran addinin Iran ya amince da kisan dubban masu zanga-zanga

    Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, A karon farko ya fito fili ya amince da cewa an kashe dubban mutane, wasu ta hanyar rashin mutuntaka da rashin tausayi, yayin zanga-zangar baya-bayan nan.

    A wani jawabi da ya yi a ranar Asabar, ya zargi Amurka da Donald Trump da alhakin kitsa zanga-zangar da ta janyo "ɓarna da kuma batanci" a ƙasarsa.

    Shugaban Amurka ya buƙaci masu zanga-zangar ƙin jinin gwamnatin Iran da su ci gaba da yin zanga-zanga, ya kuma yi barazanar ɗaukar matakin soji idan jami'an tsaro suka kashe su.

    Har yanzu daiTrump bai mayar da martani ga shugaban na Iran ba kuma BBC ta tuntubi fadar White House domin jin ta bakinsa.

    Zanga-zangar da aka yi a Iran ta yi sanadin mutuwar mutane 3,090, a cewar Kamfanin Dillancin Labarai na Hukumar Kare Hakkokin Dan Adam ta Iran (HRANA), a Amurka, a tarzomar da ta faro kan tattalin arziki a ranar 28 ga Disamba.

    Tun daga wannan lokaci zanga-zangar ta rikiɗe zuwa kiraye-kirayen kawo ƙarshen mulkin shugaban ƙasar Iran.

    Gwamnatin Iran ta bayyana zanga-zangar a matsayin tashin hankalin da maƙiyan Iran ke marawa baya.

  6. Wasu da ake zargin ƴandaba ne sun kashe mata da ƴaƴanta 6 a jihar Kano

    Wasu da ake zargin ƴan daba ne sun kashe wata matar aure da ƴaƴanta, a gidansu da sanyin safiyar ranar Asabar a jihar Kano.

    Wata sanarwa da ta fito daga ofishin mai magana da yawun rundunar ƴansandan jihar, CSP Abdullahi Haruna Kiyawa ta ce mummunan lamarin dai ya faru ne a lokacin wasu da ba a tabbatar da ko su waye ba suka afkawa Fatima Abubakar mai shekara 35 da ƴaƴanta shida, a gidansu da ke Dorayi Charanchi Quarters da muggan makamai inda suka ji masu munanan raunuka.

    Sanarwar dai ta ƙara da cewa, An kwashe waɗanda lamarin ya shafa kuma aka garzaya da su asibitin Murtala da ke Kano, inda aka tabbatar da mutuwarsu.

    Yaiyinda ta ke mi\ka ta'aziyarta ga iyalan waɗanda lamarin ya shafa, rudunar ƴansandan jihar ta bayar da tabbcin gudanar da cikakken bincike kan lamarin da niyan zaƙulo waɗanda ke da hannu a ciki.

  7. An shirya gwada lafiyar Guehi kafin komawarsa Man City

    Ɗan wasan bayan Crystal Palace Marc Guehi na ci gaba da shirin komawa Manchester City kan farashin fam miliyan 20, inda za a duba lafiyarsa ranar Lahadi.

    Guehi, mai shekara 25, ya riga ya amince da sharuɗɗan kwatiraginsa da City.

    City ta fara tattaunawa da Guehi a wannan watan sakamakon raunin da ƴan wasan baya Josko Gvardiol da Ruben Dias suka yi.

    Kwatiragin Kyaftin ɗin Crystal Palace, wanda aka alaƙanta shi da wasu manyan ƙungiyoyin Turai zai ƙare ne a bazara mai zuwa, kuma suran ƙiris ya koma Liverpool a bazarar da ta gabata.

    Guehi ya jagoranci kulob ɗin na kudancin Landan a matsayin babban kofi na farko a tarihinsa bayan da suka doke City a wasan ƙarshe na cin kofin FA a filin wasan Wembley.

    Ɗan wasan da ya fito daga ɓangaren matasan Chelsea ya buga wa Palace wasa 188 tun bayan komawarsa daga Swansea a shekarar 2020, tare da buga wasanni 33 a kakar wasa ta bana yayin da ƙungiyarsa ta fara buga gasar cin kofin Europa Conference League a karon farko.

    Zai zama babban ɗan wasa na biyu da City za ta saya a kasuwar musayar ƴan wasan nan inda tuni ta sayi Antoine Semenyo daga Bournemouth kan fam miliyan 62.5 a wannan watan.

  8. An rantsar da Mamady Doumbouya a matsayin shugaban Guinea

    An rantsar da shugaban mulkin sojan ƙasar Guinea, Janar Mamady Doumbouya a matsayin shugaban ƙasar na biyar, abin da ke nuni da abin da gwamnatin mulkin sojan ƙasar ta bayyana a matsayin komawa kan tsarin mulkin ƙasar a hukumance bayan shafe fiye da shekaru huɗu yana mulkin soja.

    Bikin rantsarwar da aka gudanar a babban filin wasa na General Lansana Conté da ke Nongo a wajen birnin Conakry, ya samu halarcin wakilan yankin da kuma masu sa ido na ƙasa da ƙasa.

    Doumbouya, mai shekaru 41, ya fara shiga siyasar Guinea cikin ban mamaki, lokacin da ya ƙwace mulki daga hannun Shugaba Alpha Condé a watan Satumba na 2021. \

    Ya zargi gwamnatin Condé da cin hanci da rashawa da wulaƙanta kundin tsarin mulki da kuma tauye haƙƙin ƴan ƙasa.

    Da ya ɗare kan karagar mulki, Doumbouya ya sha alwashin yin sauye-sauye, ciki har da yunƙurin yaƙi da cin hanci da rashawa da tsaftace ayyukan hukumomi, da kuma alƙawarin miƙa Guinea ga mulkin farar hula cikin watanni 39.

    Duk da cewa Doumbouya ya fito fili ya yi alƙawarin cewa ba zai tsaya takara ba a duk wani zaɓe da za ayi ba a nan gaba, sabon kundin tsarin mulkin da aka amince da shi a zaɓen raba gardama a bara - ya share masa hanyar yin hakan.

  9. Ƴan Denmark na zanga-zangar adawa da ƙwace Greenland

    Dubban mutane sun taru a wajen birnin Copenhagen na ƙasar Denark domin nuna adawarsu kan matakin Shugaba Trump na ƙwace iko da yankin Greenland, mallakin ƙasar.

    Masu zanga-zangar na riƙe ta kwalaye masu ɗauke da saƙonnin da ke cewa ''Ka haƙura da Greenland'', ''Greenland na ƴan yankin ne''

    Zanga-zangar na zuwa ne a daidai lokacin da wata tawagar ƴansiyasar Amurka ke ziyara a yankin, inda shugaban tawagar Sanata Chris Coons na jam'iyyar Dimokrats ya bayyana matakin na Trump a matsayin wanda bai ''dace ba''.

    A ranar Juma'a ne Mista Trump ya ce zai iya sanya haraji kan ƙasashen da suka nuna adawa da shirin nasa.

    Haka kuma shugaban na Amurka bai musanta ƙwace yankin ta ƙarfin tsiya ba.

  10. AFCON 2025: Kocin Senegel ya koka kan tsaron ƴanwasa

    Kocin Senegal Pape Bouna Thiaw ya soki matsalar rashin tsaron ƴanwasansa a lokacin da suka isa Rabat, babban birnin Moroko gabanin fafatawa a wasan ƙarshe na gasar Cin Kofin Afirka da za a gudanar ranar Lahadi a birnin.

    Bidiyoyin da aka yaɗa a shafukan intanet sun nuna yadda ƴanwasan Senegel suka ratsa ta cikin dandazon magoya baya kafin su isa wurin motarsu

    Mista Thiaw ya ce wannan ba abu ne da za a lamunta ba.

    Kawo yanzu waɗanda suka shirya gasar ba su ce komai ba game a ƙorafin.

    Senegal da Moroko ba su taɓa karawa da juna a gasar AFCON ba, don haka ake kallon wasan a matsayin wanda zai ɗauki hankali.

  11. Museveni ya lashe zaɓen Uganda karo na bakwai

    Hukumar Zaɓen Uganda ta ayyana Shugaba Yoweri Museveni a matsayin wanda ya lashe zaɓen ƙasar na ranar Alhamis.

    Da wannan sakamako Mista Museveni zai tsaiwata wa'adin mulkinsa na shekara 40 da ƙarin shekara biyar nan gaba.

    Museveni ya samu kashi 72 na ƙuri'un da aka kaɗa, yayin da jagoran adawar ƙasar Bobi Wine ya samu kashi 25 a cewar hukumar zaɓen.

    Bobi Wine ya yi watsi da sakamakon inda ya bayyana shi da ''ƙarya'', tare da kiran ƴan ƙasar su yi zanga-zangar lumana don nuna adawa da sakamakon.

    Museveni, mai shekara 81, ya fara zama shugaban ƙasar a matsayin jagoran ƴantawaye a 1986, kuma daga nan ya riƙa lashe duka zaɓukan ƙasar da aka yi.

    An samu tashe-tashen hankula a zaɓen, inda Bobi Wine ya ce mutum 21 aka kashe a rikicin.

    Sai dai kawo yanzu mutum bakwai hukumomi suka tabbatar da mutuwarsu.

    Tun a ranar Talata aka katse intanet a ƙasar, wani abu da ya haifar da wahalar tantance sahihancin bayanai.

    Hukumomi dai sun kare matakin hana yaɗuwar labaran ƙarya, da aikata zamba da rura rikici, matakin da Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Majalisar Dinkin Duniya ta yi tir da shi.

  12. Ƴansiyasar Amurka sun ce akwai damuwa kan yunƙurin ƙwace Greenland

    Ƴansiyasar Amurka da ke ziyara a Denmark sun ce akwai damuwa a ƙasar da kuma yankin Greenland sakamakon nanata ƙwace yankin da Shugaba Trump ke cewa Amurka za ta yi.

    Yayin da yake jawabi a birnin Copenhagen shugaban tawagar Sanata Chris Coons, na jam'iyyar Dimokrat ya ce kalaman na Mista Trump na ƙara dagula lamurra.

    A ranar Juma'a ne Shugaban na Amurka ya yi gargaɗin sanya ƙarin haraji ga ƙasashen da suka nuna adawa da shirin nasa.

    Mista Trump bai musanta ƙwace yankin da ƙarfi ba, yana mai cewa tsibirin na da matuƙar muhimmanci ga tsaron Amurka.

    Mista Coons ya ce Denmark babbar ƙawa ce ga ƙungiyar NATO, kuma idan Trump ya ci gaba da shirin nasa Amurka za ta rasa ƙawanyen da yawa.

  13. Amurka za ta aika ƴansama jannati zuwa duniyar wata

    Hukumar kula da sararin samaniyar Amurka, NASA ta fara shirye-shiryen aika mutane zuwa duniyar wata karon farko cikin fiye da shekara 50.

    Tafiyar ta kwana 10 za ta ƙunshi ƴansama jannati huɗu zuwa duniyar wata a wani shiri a yunƙurin sauka a duniyar watan.

    Tuni aka fito da kumbon da zai ɗauki mutanen - mai tsawon mita 100 - daga cibiyar NASA da ke Cape Canaveral a jihar Florida zuwa cibiyar harba kumbo da ke Kennedy Space.

    Zai ɗauki sa'o'i 12 kafin a kai shi cibiyar da kammala gwaje-gwajen da za a yi kafin harba shi.

    Ana sa ran harba kumbo ranar 6 ga watan Fabrairun da ke tafe.

  14. Trump ne ya janyo mutuwar masu zanga-zanga a Iran - Ayatollah Khamenei

    Jagoran Addinin Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce Shugaba Trump na Amurka ne ya janyo mutuwar masu zanga-zangar da ta ɓarke a ƙasar a baya-bayan nan.

    Ya ce Iran na ɗaukar Trump a matsayin babban mai laifi saboda sanya bakinsa cikin tashin hankalin.

    Ayatollah Khamenei ya zargi mutanen - da ke da alaƙa da Isra'ila da Amurka - wajen kashe dubban fararen hula da jami'an tsaro.

    Ya ƙara da cewa ba wanda ya isa ya jefa Iran cikin yaƙi, amma dole ne masu laifi na cikin gida da na ƙetare su fuskanci hukunci.

  15. Ƴanbindiga 80 sun miƙa wuya ƙarƙashin shirin afuwa na jihar Cross River

    Rundunar sojin Najeriya ta samu gagarumar nasara a yaƙin da suke yi a ayyukan ƴanbindiga bayan da wasu gomman masu ɗauke da makamai suka miƙa wuya bisa raɗin kai ƙarƙashin shirin afuwa da gwamnatin jihar Cross Rivers ta ɓullo da shi.

    Cikin wata sanarwa da rundunar sojin ta wallafa a shafinta na X a ranar Juma'a ta ce aƙalla ƴanbindiga 80 da ke ayyukan satar mai a cikin teku suka miƙa kansu tare da ajiye makaman karƙashin shirin afuwar gwamnatin jihar da ke kudu maso kudancin ƙasar.

    Rahotonni sun ce yanbindigar sun isa wurin shirin afuwar daga sansanoni biyu, na farko ƙarƙashin jagorancin ThankGod Ebikontei, da aka fi sani da Ayibanuagha, wanda ya gabatar da mayaƙa 39.

    Sai kuma dabar John Isaac, da aka fi sani da Akpokolo mai jagorantar dabar da ake yi wa laƙabi da Border Boys, wanda ya gabatar da mayaƙa 41.

    A lokacin miƙa wuyan ƴanbindigar sun miƙa makamansu da suka haɗa da ƙirar AK-47 da masu jigida da sauran nau'ikan bindigogi da nau'ikan harsasai daban-daban da jiragen ruwa uku masu tsananin gudu da sauran kayayyakinsu.

    Yayin da yake jawabi a wajen shirin afuwar babban kwamandan runduna ta 13 ta sojin Najeriya da ke yankin, Birgediya Janar PO Alimikhena, ya bayyana miƙa wuyan a matsayin ''gagarumin ci gaba''.

  16. Bobi Wine ya ce yana ɓoye a wani wuri bayan 'kuɓuta daga kamu'

    Jagoran adawar Uganda, Bobi Wine ya ce yana ɓoye a wani wuri bayan kuɓuta daga wani abu da ya bayyana da samamen jami'an tsaro a gidansa da ke birnin Kampala

    Ya ce matarsa da sauran iyalansa na ƙarƙashin ɗaurin talala, inda aka datse hanyoyin zuwa gidansa

    Ƴansanda sun musanta iƙirarin nasa, suna masu cewa Wine yana cikin gidansa, kuma an taƙaita zuwa gidansa ne saboda dalilai na tsaro.

    Tun da farko jam'iyyarsa ta ce jami'an tsaro sun fitar da shi daga gidansa ta tilas zuwa wani wuri da ba a sani ba.

    Wine ya yi watsi da sakamakon farko na zaɓen shugaban ƙasar da ya nuna Shugaba Yoweri Museveni na kan gaba da gagarumar tazara a ƙoƙarinsa na komawa mulkin ƙasar a wa'adi na bakwai.

    Nan gaba a yau ne a ake sa ran bayyana cikakken sakamakon zaɓen.

  17. Gwamnatin Legas za ta binciki mutuwar wasu tagwaye bayan yi musu riga-kafi

    Gwamnatin jihar Legas ta bayar da umarnin gudanar da binciken musabbabin mutuwar wasu tagwaye, waɗanda aka bayar da rahoton mutuwarsu kwana guda bayan yi musu allurar riga-kafi a wata cibiyar allurar da ke jihar.

    Lamarin ya ɗauki hankali ne bayan da mahaifin yaran mai suna Samuel Alozie - da aka fi sani da Promise Samuel a dandalin TikTok - ya wallafa bidiyon gawarwakin tagwayen yayin da yake bayyana yadda suka mutu bayan yi musu riga -kafin.

    Daga baya kuma ya sake wallafa wani bidiyo inda yake cewa a ranar 24 ga watan Disamban da ya gabata sun kai tagwayen riga-kafi ne kamar yadda suka saba kai su a baya, sai dai ya ce a wannan karon yaran sun jigata bayan yi musu riga-kafin.

    “Ba sa iya cin abinci, ba sa yin wasa, ba ma sa rigimar da suka saba yi a baya, sun kasance cikin kasala,'' in ji shi.

    Ya ci gaba da cewa ma'aikatan lafiyar da suka yi riga-kafin sun ce a ba su maganin zazzaɓi idan jikinsu ya yi ɗumi, abin da kuma ya ce sun yi shi mahaifiyarsu, har ma wanka suka yi musu da ruwan sanyi domin jikin nasu na sauka daga zafin zazzaɓin amma hakan ba ta samu ba.

    Inda ya ce daga ƙarshe duka yaran biyu suka mutu bayan kwana guda da yi musu zazzaɓin.

    Lamarin ya sake tasowa ne bayan mutuwar ɗaya daga cikin tagawayen fitacciyar marubuciyar nan Chimamanda Adichie, wadda ta zargi asibiti da sakacin mutuwar ɗan nata.

    Zargin jami'an lafiya da sakaci wajen mutuwar marasa lafiya ya jima yana karakaina tsakanin wasu ƴan ƙasar.

    Ko a makon da ya gabata ma hukumomi a jihar Kano sun dakatar da wasu likitoci bayan da suka manta alkamashin tiyata a cikin wata mata, lamarin da ya kai ga mutuwarta.

  18. MDD ta yi gargaɗin ƙaruwar yunwa a Najeriya saboda janye tallafi

    Shirin Samar da Abinci na Majalisar Dinkin Duniya ya yi gargaɗin cewa dubban mutane na fuskantar barazanar faɗawa ƙangin yunwar da ba a taɓa ganin irinta ba cikin shekara 10 a arewa maso gabashin Najeriya, sakamakon janye tallafi daga ƙungiyoyin duniya.

    WFP ya ce a jihar Borno kawai kusan mutum 15,000 ne ke cikin barazanar, yayin da aka yi hasashen samun ƙananan yara miliyan 13 da za su fuskanci matsalar tamowa a yankin arewa maso gabashin.

    Rikice-rikice da tilasta wa mutane barin gidajensu da matsalar tattalin arziki na daga cikin abubuwan da ke haddasa rashin wadataccen abinci a yankin.

    To sai dai a wannan shekara janyewar tallafi daga ƙungiyoyin duniya ta tsananta matsalar kamar yadda WFP ya bayyana cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma'a.

    “Mun ga yadda samun raguwar tallafin a 2025 ya tsananta yunwa da tamowa a yankin,'' a cewar Sarah Longford, mataimakiyar daraktar WFP ta yakin yammaci da tsakiyar Afirka.

    WFP ta ce aƙalla mutum miliyan 55 ne ke fuskantar barazanar ƙarancin abinci a yammaci da tsakiyar Afirka, yayin da fiye da kashi uku cikin huɗu na wannan adadi ke ƙasashen Najeriya da Kamaru da Chadi da kuma Nijar.

  19. Kotu ta bayar da umarnin dakatar da yunƙurin tsige Fubara

    Wata babbar kotun Rivers ta bayar da wani umarnin wucin-gadi na dakatar da yunƙurin tsige gwamnan jihar Siminalayi Fubara da mataimakiyarsa Ngozi Nma-Odu.

    Cikin hukuncin da ta bayar a birnin Fatakwal, kotun ta dakatar da kakakin majalisar dokokin jihar, Martin Amaewhule da wasu mutane da ake ƙara - ciki har da akawun majalisar da alƙalin alƙalan jihar - daga yunƙurin tsige gwamnan, kamar yadda Gudan talbijin na Channels ya ruwaito.

    Haka kuma kotun ta bayar da wani keɓantaccen umarni na hana alƙalin alkalan jihar, Mai Shari'a Simeon Chibuzor-Amadi, karɓar wani ƙorafi ko miƙa shi ko kuma duba wata buƙata ko shawara da ta jiɓanci batun tsige gwamnan daga majalisar dokokin jihar, har zuwa nan da kwana bakwai, kamar yadda hukuncin kotun ya nuna.

    Gwamnan jihar da mataimakiyarsa ne suka shigar da ƙarar daban-daban a gaban kotun, don neman wannan buƙata.

    Jihar Ribas dai na fama da rikicin siyasa tun bayan zaɓen 2023, lamarin da ya kai ga Shugaba Tinubu dakatar da gwamnan na tsawon wata shida a shekarar da ta gabata.

  20. 'Babu alaƙa tsakanin shan Paracetamol da haihuwar jarirai masu galahanga'

    Wani binciken lafiya ya gano cewa babu alaƙa tsakanin shan maganin zazzaɓi na Paracetamol ga mata masu juna biyu da kuma haihuwar jarirai masu lalurar galahanga ko (autism) ko wata nakasasa.

    Sakamakon binciken ya sha bamban da iƙirarin da Shugaba trump na Amurka ya yi bara da yake cewa mata masu juna biyu su guji shan maganin.

    Masu binciken sun yi nazari mai zurfi, inda suka yi binciken a kan dubban mata masu juna biyu a Amurka.

    Sun ce ya kamata a tabbatar wa dubban mata cewa za su iya shan paracetamol idan suna da juna-biyu.

    Tuni dai ma'aikatar lafiyar Amurka ta yi watsi da sokamakon binciken.