KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Asabar 17/01/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, Asabar 17/01/2026

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Daga Abdullahi Bello Diginza

  1. Museveni ya lashe zaɓen Uganda karo na bakwai

    Shugaban Uganda

    Asalin hoton, AFP via Getty Images

    Bayanan hoto, Yoweri Museveni ya fara ɗarewa karagar mulkin Uganda a 1986 a matsayin shugaban ƴantawaye

    Hukumar Zaɓen Uganda ta ayyana Shugaba Yoweri Museveni a matsayin wanda ya lashe zaɓen ƙasar na ranar Alhamis.

    Da wannan sakamako Mista Museveni zai tsaiwata wa'adin mulkinsa na shekara 40 da ƙarin shekara biyar nan gaba.

    Museveni ya samu kashi 72 na ƙuri'un da aka kaɗa, yayin da jagoran adawar ƙasar Bobi Wine ya samu kashi 25 a cewar hukumar zaɓen.

    Bobi Wine ya yi watsi da sakamakon inda ya bayyana shi da ''ƙarya'', tare da kiran ƴan ƙasar su yi zanga-zangar lumana don nuna adawa da sakamakon.

    Museveni, mai shekara 81, ya fara zama shugaban ƙasar a matsayin jagoran ƴantawaye a 1986, kuma daga nan ya riƙa lashe duka zaɓukan ƙasar da aka yi.

    An samu tashe-tashen hankula a zaɓen, inda Bobi Wine ya ce mutum 21 aka kashe a rikicin.

    Sai dai kawo yanzu mutum bakwai hukumomi suka tabbatar da mutuwarsu.

    Tun a ranar Talata aka katse intanet a ƙasar, wani abu da ya haifar da wahalar tantance sahihancin bayanai.

    Hukumomi dai sun kare matakin hana yaɗuwar labaran ƙarya, da aikata zamba da rura rikici, matakin da Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Majalisar Dinkin Duniya ta yi tir da shi.

  2. Ƴansiyasar Amurka sun ce akwai damuwa kan yunƙurin ƙwace Greenland

    Ƴansiyasar Amurka da ke ziyara a Denmark sun ce akwai damuwa a ƙasar da kuma yankin Greenland sakamakon nanata ƙwace yankin da Shugaba Trump ke cewa Amurka za ta yi.

    Yayin da yake jawabi a birnin Copenhagen shugaban tawagar Sanata Chris Coons, na jam'iyyar Dimokrat ya ce kalaman na Mista Trump na ƙara dagula lamurra.

    A ranar Juma'a ne Shugaban na Amurka ya yi gargaɗin sanya ƙarin haraji ga ƙasashen da suka nuna adawa da shirin nasa.

    Mista Trump bai musanta ƙwace yankin da ƙarfi ba, yana mai cewa tsibirin na da matuƙar muhimmanci ga tsaron Amurka.

    Mista Coons ya ce Denmark babbar ƙawa ce ga ƙungiyar NATO, kuma idan Trump ya ci gaba da shirin nasa Amurka za ta rasa ƙawanyen da yawa.

  3. Amurka za ta aika ƴansama jannati zuwa duniyar wata

    Kumbo

    Asalin hoton, NASA

    Hukumar kula da sararin samaniyar Amurka, NASA ta fara shirye-shiryen aika mutane zuwa duniyar wata karon farko cikin fiye da shekara 50.

    Tafiyar ta kwana 10 za ta ƙunshi ƴansama jannati huɗu zuwa duniyar wata a wani shiri a yunƙurin sauka a duniyar watan.

    Tuni aka fito da kumbon da zai ɗauki mutanen - mai tsawon mita 100 - daga cibiyar NASA da ke Cape Canaveral a jihar Florida zuwa cibiyar harba kumbo da ke Kennedy Space.

    Zai ɗauki sa'o'i 12 kafin a kai shi cibiyar da kammala gwaje-gwajen da za a yi kafin harba shi.

    Ana sa ran harba kumbo ranar 6 ga watan Fabrairun da ke tafe.

  4. Trump ne ya janyo mutuwar masu zanga-zanga a Iran - Ayatollah Khamenei

    Ayatollah

    Asalin hoton, EPA

    Jagoran Addinin Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce Shugaba Trump na Amurka ne ya janyo mutuwar masu zanga-zangar da ta ɓarke a ƙasar a baya-bayan nan.

    Ya ce Iran na ɗaukar Trump a matsayin babban mai laifi saboda sanya bakinsa cikin tashin hankalin.

    Ayatollah Khamenei ya zargi mutanen - da ke da alaƙa da Isra'ila da Amurka - wajen kashe dubban fararen hula da jami'an tsaro.

    Ya ƙara da cewa ba wanda ya isa ya jefa Iran cikin yaƙi, amma dole ne masu laifi na cikin gida da na ƙetare su fuskanci hukunci.

  5. Ƴanbindiga 80 sun miƙa wuya ƙarƙashin shirin afuwa na jihar Cross River

    ƴanbindiga

    Asalin hoton, Nigerian Army/X

    Rundunar sojin Najeriya ta samu gagarumar nasara a yaƙin da suke yi a ayyukan ƴanbindiga bayan da wasu gomman masu ɗauke da makamai suka miƙa wuya bisa raɗin kai ƙarƙashin shirin afuwa da gwamnatin jihar Cross Rivers ta ɓullo da shi.

    Cikin wata sanarwa da rundunar sojin ta wallafa a shafinta na X a ranar Juma'a ta ce aƙalla ƴanbindiga 80 da ke ayyukan satar mai a cikin teku suka miƙa kansu tare da ajiye makaman karƙashin shirin afuwar gwamnatin jihar da ke kudu maso kudancin ƙasar.

    ƴanbindiga

    Asalin hoton, Nigerian Army/X

    Rahotonni sun ce yanbindigar sun isa wurin shirin afuwar daga sansanoni biyu, na farko ƙarƙashin jagorancin ThankGod Ebikontei, da aka fi sani da Ayibanuagha, wanda ya gabatar da mayaƙa 39.

    Sai kuma dabar John Isaac, da aka fi sani da Akpokolo mai jagorantar dabar da ake yi wa laƙabi da Border Boys, wanda ya gabatar da mayaƙa 41.

    Makamai

    Asalin hoton, Nigerian Army/X

    A lokacin miƙa wuyan ƴanbindigar sun miƙa makamansu da suka haɗa da ƙirar AK-47 da masu jigida da sauran nau'ikan bindigogi da nau'ikan harsasai daban-daban da jiragen ruwa uku masu tsananin gudu da sauran kayayyakinsu.

    Yayin da yake jawabi a wajen shirin afuwar babban kwamandan runduna ta 13 ta sojin Najeriya da ke yankin, Birgediya Janar PO Alimikhena, ya bayyana miƙa wuyan a matsayin ''gagarumin ci gaba''.

    Makamai

    Asalin hoton, Nigerian Army/X

  6. Bobi Wine ya ce yana ɓoye a wani wuri bayan 'kuɓuta daga kamu'

    Jagoran adawar Uganda, Bobi Wine ya ce yana ɓoye a wani wuri bayan kuɓuta daga wani abu da ya bayyana da samamen jami'an tsaro a gidansa da ke birnin Kampala

    Ya ce matarsa da sauran iyalansa na ƙarƙashin ɗaurin talala, inda aka datse hanyoyin zuwa gidansa

    Ƴansanda sun musanta iƙirarin nasa, suna masu cewa Wine yana cikin gidansa, kuma an taƙaita zuwa gidansa ne saboda dalilai na tsaro.

    Tun da farko jam'iyyarsa ta ce jami'an tsaro sun fitar da shi daga gidansa ta tilas zuwa wani wuri da ba a sani ba.

    Wine ya yi watsi da sakamakon farko na zaɓen shugaban ƙasar da ya nuna Shugaba Yoweri Museveni na kan gaba da gagarumar tazara a ƙoƙarinsa na komawa mulkin ƙasar a wa'adi na bakwai.

    Nan gaba a yau ne a ake sa ran bayyana cikakken sakamakon zaɓen.

  7. Gwamnatin Legas za ta binciki mutuwar wasu tagwaye bayan yi musu riga-kafi

    Gwamnan Legas

    Asalin hoton, Babajide Sanwo-Olu/X

    Gwamnatin jihar Legas ta bayar da umarnin gudanar da binciken musabbabin mutuwar wasu tagwaye, waɗanda aka bayar da rahoton mutuwarsu kwana guda bayan yi musu allurar riga-kafi a wata cibiyar allurar da ke jihar.

    Lamarin ya ɗauki hankali ne bayan da mahaifin yaran mai suna Samuel Alozie - da aka fi sani da Promise Samuel a dandalin TikTok - ya wallafa bidiyon gawarwakin tagwayen yayin da yake bayyana yadda suka mutu bayan yi musu riga -kafin.

    Daga baya kuma ya sake wallafa wani bidiyo inda yake cewa a ranar 24 ga watan Disamban da ya gabata sun kai tagwayen riga-kafi ne kamar yadda suka saba kai su a baya, sai dai ya ce a wannan karon yaran sun jigata bayan yi musu riga-kafin.

    “Ba sa iya cin abinci, ba sa yin wasa, ba ma sa rigimar da suka saba yi a baya, sun kasance cikin kasala,'' in ji shi.

    Ya ci gaba da cewa ma'aikatan lafiyar da suka yi riga-kafin sun ce a ba su maganin zazzaɓi idan jikinsu ya yi ɗumi, abin da kuma ya ce sun yi shi mahaifiyarsu, har ma wanka suka yi musu da ruwan sanyi domin jikin nasu na sauka daga zafin zazzaɓin amma hakan ba ta samu ba.

    Inda ya ce daga ƙarshe duka yaran biyu suka mutu bayan kwana guda da yi musu zazzaɓin.

    Lamarin ya sake tasowa ne bayan mutuwar ɗaya daga cikin tagawayen fitacciyar marubuciyar nan Chimamanda Adichie, wadda ta zargi asibiti da sakacin mutuwar ɗan nata.

    Zargin jami'an lafiya da sakaci wajen mutuwar marasa lafiya ya jima yana karakaina tsakanin wasu ƴan ƙasar.

    Ko a makon da ya gabata ma hukumomi a jihar Kano sun dakatar da wasu likitoci bayan da suka manta alkamashin tiyata a cikin wata mata, lamarin da ya kai ga mutuwarta.

  8. MDD ta yi gargaɗin ƙaruwar yunwa a Najeriya saboda janye tallafi

    Buhunan Abinci

    Asalin hoton, others

    Shirin Samar da Abinci na Majalisar Dinkin Duniya ya yi gargaɗin cewa dubban mutane na fuskantar barazanar faɗawa ƙangin yunwar da ba a taɓa ganin irinta ba cikin shekara 10 a arewa maso gabashin Najeriya, sakamakon janye tallafi daga ƙungiyoyin duniya.

    WFP ya ce a jihar Borno kawai kusan mutum 15,000 ne ke cikin barazanar, yayin da aka yi hasashen samun ƙananan yara miliyan 13 da za su fuskanci matsalar tamowa a yankin arewa maso gabashin.

    Rikice-rikice da tilasta wa mutane barin gidajensu da matsalar tattalin arziki na daga cikin abubuwan da ke haddasa rashin wadataccen abinci a yankin.

    To sai dai a wannan shekara janyewar tallafi daga ƙungiyoyin duniya ta tsananta matsalar kamar yadda WFP ya bayyana cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma'a.

    “Mun ga yadda samun raguwar tallafin a 2025 ya tsananta yunwa da tamowa a yankin,'' a cewar Sarah Longford, mataimakiyar daraktar WFP ta yakin yammaci da tsakiyar Afirka.

    WFP ta ce aƙalla mutum miliyan 55 ne ke fuskantar barazanar ƙarancin abinci a yammaci da tsakiyar Afirka, yayin da fiye da kashi uku cikin huɗu na wannan adadi ke ƙasashen Najeriya da Kamaru da Chadi da kuma Nijar.

  9. Kotu ta bayar da umarnin dakatar da yunƙurin tsige Fubara

    Gwamman Rivers

    Asalin hoton, Siminalayi Fubara/X

    Wata babbar kotun Rivers ta bayar da wani umarnin wucin-gadi na dakatar da yunƙurin tsige gwamnan jihar Siminalayi Fubara da mataimakiyarsa Ngozi Nma-Odu.

    Cikin hukuncin da ta bayar a birnin Fatakwal, kotun ta dakatar da kakakin majalisar dokokin jihar, Martin Amaewhule da wasu mutane da ake ƙara - ciki har da akawun majalisar da alƙalin alƙalan jihar - daga yunƙurin tsige gwamnan, kamar yadda Gudan talbijin na Channels ya ruwaito.

    Haka kuma kotun ta bayar da wani keɓantaccen umarni na hana alƙalin alkalan jihar, Mai Shari'a Simeon Chibuzor-Amadi, karɓar wani ƙorafi ko miƙa shi ko kuma duba wata buƙata ko shawara da ta jiɓanci batun tsige gwamnan daga majalisar dokokin jihar, har zuwa nan da kwana bakwai, kamar yadda hukuncin kotun ya nuna.

    Gwamnan jihar da mataimakiyarsa ne suka shigar da ƙarar daban-daban a gaban kotun, don neman wannan buƙata.

    Jihar Ribas dai na fama da rikicin siyasa tun bayan zaɓen 2023, lamarin da ya kai ga Shugaba Tinubu dakatar da gwamnan na tsawon wata shida a shekarar da ta gabata.

  10. 'Babu alaƙa tsakanin shan Paracetamol da haihuwar jarirai masu galahanga'

    maganin PCM

    Asalin hoton, Getty Images

    Wani binciken lafiya ya gano cewa babu alaƙa tsakanin shan maganin zazzaɓi na Paracetamol ga mata masu juna biyu da kuma haihuwar jarirai masu lalurar galahanga ko (autism) ko wata nakasasa.

    Sakamakon binciken ya sha bamban da iƙirarin da Shugaba trump na Amurka ya yi bara da yake cewa mata masu juna biyu su guji shan maganin.

    Masu binciken sun yi nazari mai zurfi, inda suka yi binciken a kan dubban mata masu juna biyu a Amurka.

    Sun ce ya kamata a tabbatar wa dubban mata cewa za su iya shan paracetamol idan suna da juna-biyu.

    Tuni dai ma'aikatar lafiyar Amurka ta yi watsi da sokamakon binciken.

  11. Ɗan Bobi Wine ya ce jami'an tsaro sun 'ɗauke' iyayensa

    Bobi Wine

    Asalin hoton, Getty Images

    Ɗangidan jagoran adawar Uganda ya ce sojoji da wasu jami'an tsaro na musamman sun sace iyayensa daga gidansu da ke Kampala.

    Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafin sa na X, Solomon Kampala ya ce an ''ɗauke Bobi Wine da Barbara Kyagulanyi tare da kai su wani ɓoyayyen wuri.

    Wani makusancin Wine ya shaida wa BBC cewa jami'an tsaron sun shiga gidansa da ƙarfin tsiya sannan suka ɗauke a wani jirgi mai saukar ungulu.

    Tun farko Bobi Wine ya soki ingancin sakamkon farko na zaɓen shugaban ƙasar da ya gudana ranar Alhamis, wanda ya nuna Shugaba Yoweri Museveni ne ke kan gaba da gagarumar tazara, yayin da aka kusan kammala ƙirga ƙuri'u.

    Sai dai rundunar ƴansandan ƙasar ta musanta iƙirarin sace Wine.

    A yau Alhamis ne ake sa ran bayyana sakamkon zaɓen, wanda tuni ake hasashen Museveni ne zai lashe.

  12. Trump na naɗa kwamitin zaman lafiya da zai jagoranci Gaza

    Donald Trump

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban Amurka, Donbald Trump ya bayyana sunayen mambobin kwamitin da zai jagoranta, wanda zai tafiyar da zaman lafiyar Gaza.

    Daga cikin mambobin kwamitin har da sakataren harkokin wajen Amurka, Marco Rubio da tsohon firaministan Birtaniya Tony Blair.

    Sauran sun haɗa da surukinsa, Jared Kushner da kuma wakilin Trump na musamman a Gabas ta Tsakiya, Steve Witkoff da shugaban Bankin Duniya, Ajay Banga.

    Fadar gwamnatin Amurka ta ce akwai aikin musamman da kowane ɗaya daga cikin mambobin kwamitin zai yi, don taimaka wa zaman lafiyar Gaza.

    Shugaba Trump ne zai jagoranci kwamitin, yayin da wasu ƙwararrun ƴan Boko za su kula da kwamitin farar hula a Gaza.

  13. Assalamu alaikum

    Masu bin shafin BBC Hausa kai-tsaye barkanmu da safiyar wannan rana ta Asabar.

    Abdullahi Bello Diginza ke fatan kasancewa da ku a daidai wannan lokaci domin kawo muku halin da duniya ke ciki.

    Ku biyo a shafukanmu na sada zumunta, domin tafka muhawara kan labaran da muke wallafawa.