Najeriya za ta kara da Afirka ta Kudu a wasan neman gurbin kofin duniya

Asalin hoton, Getty Images
Tawagar Super Eagles ta Najeriya za ta kara da Afirka ta Kudu da Benin da Rwanda da Zimbabwe da kuma Lesotho a wasan rukuni na uku na gasar cin kofin duniya da za a yi a shekara ta 2026.
A ranar Alhamis ne aka gudanar da bikin fitar da jadawalin wasannin a birnin Abidjan na ƙasar Ivory Coast.
Sau 14 dai kasashen Najeriya da Afirka ta Kudu suka fafata tsakanin su, inda Super Eagles ta yi nasara sau bakwai sannan suka yi canjaras biyu.
A karo na ƙarshe da Najeriya ta kara da Bafana Bafana a wasan neman tikitin shiga gasar cin kofin duniya shi ne kafin gasar 2010.
Super Eagles ta samu nasara a wasanni biyu da suka fafata, amma Afirka ta Kudu ta samu gurbin shiga gasar la’akari da matsayin mai masaukin baki.
Senegal, zakarun Afirka, na rukunin na biyu ne tare da Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango da Togo da Mauritania da Sudan da kuma Sudan ta Kudu.
Morroco - wadda ta kai wasan dab da ƙarshe a gasar Kofin Duniya da aka buga a Qatar - ta samu kanta a rukuni na biyar inda za ta kara da Zambia da Tanzaniada Congo Brazzaville da Jamhuriyar Nijar da kuma Eritrea.
Ghana tana rukuni na daya tare da Mali, da Madagascar da Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya, da Comoros da kuma Chadi.
Cikakken jaddawalin
Yanzu za ku iya samun labaran BBC Hausa kai-tsaye a wayoyinku.
Latsa nan domin shiga
Karshen Whatsapp
Rukuni na A: Masar, Burkina Faso, Guinea-Bissau, Saliyo, Ethiopia, da kuma Djibouti
Rukuni na B: Senegal, Democratic Republic of Congo, Togo, Mauritania, Sudan da kuma Southern Sudan
Rukuni na C: Najeriya, Afirka ta Kudu, Benin Republic, Zimbabwe, Rwanda da kuma Lesotho
Rukuni na D: Kamaru, Cape Verde, Angola, Libya, Eswatini da kuma Mauritius
Rukuni na E: Morroco, Zambia, Tanzania, Congo Brazzaville, Nijar da Eritrea.
Rukuni na F: Ivory Coast, Gabon, Kenya, Gambia, Burundi, da kuma Seychelles
Rukuni na G: Algeria, Guinea, Uganda, Mozambique, Botswana, Somalia
Rukuni na H: Tunisia, Equatorial Guinea, Namibia, Malawi, Liberia, Sao Tome e Principe
Rukuni na I: Ghana, Mali, Madagascar, the Central African Republic, Comoros and Chad.
Za a fara buga wasannin daga ranar 3 ga watan Nuwamban 2023, zuwa ranar 18 ga watan Nuwamban 2025.
Kasashen Afirka na da gurbi tara, bayan da aka kara adadin kasashen da za su shiga gasar da za a buga a shekarar 2026 zuwa 48.
Za dai a buga gasar a kasashen Amurka da Mexico da kuma Canada daga ranar 11 ga watan Yuni zuwa 19 ga watan Yulin 2026.
Kasar Argentina ce dai ke rike da kofin gasar da ta dauka a shekarar 2022 da aka buga a Qatar













